ALLAHU Akbar! Allah ya yi wa wani yaro mai kimanin shekaru 15 ɗan fitaccen mawaƙi Abubakar Yarima rasuwa.
Yaron, Muhammad Sani (Garkuwa), ya rasu ne da yamma a ranar Lahadi, 10 ga Afrilu, 2022, sanadiyyar shiga Kogin Kaduna da ya yi.
Alhaji Abubakar Yarima ya shaida wa mujallar Fim yadda abin ya faru, ya ce, “Bayan ruwan sama da aka yi a ranar Juma’a, 8 ga Afrilu, kasancewa ruwan shi ne na farko a Kaduna, wannan ya sa su ka tafi kamun ki fi a washegari, wanda ni da iyayen su mata ba mu sani ba. Ka san a Kinkinau mu ke da zama, kuma akwai Kogin Kaduna ta unguwar.

“A ranar farko an ce sun je da abokan, sun yi wanka. Shi aka ce ya shiga, sai ya ƙi shiga. Da su ka dawo sai su ka shiga maƙwabta, a nan su ka gyara kifin su da su ka kamo su ka ci.
“An ce wata daga cikin maƙwabtan ne ta ba su dukkan abin da su ka yi amfani da shi, sai dai ni ban gamsu da maganar ba. In ma da gaske ne, ta yi kuskure. Kamata ya yi ta faɗa wa iyayen su don a tsawatar masu.”
Yarima ya ƙara da cewa, “Garkuwa shi ne ɗa na na biyar a cikin ‘ya’ya na. Saboda halin rayuwa, idan ina gida duk yadda aka yi mintuna goma ban gan shi ba sai na sa an kira mani shi, don ba na son ya na yin nisa.”
Ya ce a ranar da aka yi rasuwar ma ba ya gida. Ya ce: “Game da yadda na samu labarin lamarin, ba na gida, gwamnan Zamfara ya kira ni ya sa ni wani aiki. Da yamma aka kira ni ake ce mani wani yaro ya faɗa ruwa, ga ma rigar sa nan shi ba a gan shi ba. Na ce a siffanta mani kamannin sa. Aka faɗa mani, sai na ce shi ne.
“Na zo da kai na na shiga ruwan ban gan shi ba. Sai mu ka yi wa wasu masunta magana, su ka yi mana kwatance wasu da cewa su ke yin irin wannan binciken.

“Kafin mu je gare su, wasu yara su ka shiga su ka fito da shi a mace. Mu ka ɗauke shi a mota, mu ka koma gida, aka yi masa jana’iza yadda addinin Musulunci ya tanada.”
To, Allah ya jiƙan Muhammad Sani (Garkuwa), amin.