• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zaɓen 2023: INEC ta kafa wa ‘yan jarida dokokin hana su fifita wata jam’iyya kan wata

by DAGA WAKILIN MU
October 1, 2022
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu

Farfesa Mahmood Yakubu

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR  Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fayyace wa kafafen yaɗa labarai dokoki da ƙa’idojin bai wa jam’iyyun siyasa lokuta daidai da juna a yayin ba da labaran kamfen.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ya yi masu wannan bayani dalla-dalla, lokacin da ya ke jawabi wajen taron ƙara wa kafafen yaɗa labarai na talbijin da rediyo ilmin sanin makamar yayata jam’iyyun siyasa a yayin kamfen.

An shirya taron ne a cikin makon nan a Abuja domin ƙara ɗora su kan hanyoyin da doka ta tanadar wajen tabbatar da bin ƙa’ida yayin yaƙin neman zaɓen 2023.

A ranar 28 ga Satumba ne INEC ta amince aka fara kamfen, kamar yadda Sashe na 94 (1) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.

Ya ce: “Yayin da za a fara yaƙin neman zaɓen 2023, ya na da muhimmanci dukkan jam’iyyu, ‘yan takara, magoya bayan su da kafafen yaɗa labarai su sani cewa su na da muhimmiyar rawa da za su taka wajen tabbatar da an gudanar da komai bisa yadda doka ta gindaya.

“Kada a riƙa yayata kalaman ƙiyayya, zage-zage, sakin baki, kalaman tunzura jama’a ko harzuƙa wani ɗan takara, aibantawa ko muzantawa, cin zarafi, lahanta wani ko lalata kayan kamfen ɗin wata jam’iyya.

“Sashe na 95 na Dokar Zaɓe ta 2022 ya fayyace komai dangane da ƙa’idojin da ba a yarda a karya ba.

“Mun sha samun ƙorafe-ƙorafen hana jam’iyyun adawa samun damar yin amfani da kayayyaki mallakar gwamnati, kamar kafafen yaɗa labarai ko filayen yin kamfen.

“Ina jaddada cewa yin amfani da ƙarfin mulki a hana jam’iyyar adawa dama daidai da jam’iyya mai mulki a kafafen yaɗa labarai na gwamnati haramun ne a dokar INEC Sashe na 95 (2,3,4,5,6).

“Kada kafafen yaɗa labarai na gwamnati su hana wata jam’iyya damar yayata manufofin ta daidai da lokacin da su ka bai wa jam’iyya mai mulki.”

Yakubu ya ce akwai hukuncin da dokar INEC ta tanadar ga kafar yaɗa labaran, wanda ya haɗa da cin tara ta naira miliyan biyu. 

“Amma idan aka sake karya dokar, to sai an biya naira miliyan biyar. Shi kuma shugaban kafar yaɗa labarai ko ma’aikatan da su ka karya dokar za a ci su tara ta naira miliyan ɗaya, ko ɗaurin wata shida a kurkuku.”

Loading

Previous Post

Tsohuwar matar Adam Zango, Maryam A.B. Yola, ta yi auren cin amana, inji jarumar Kannywood Sapna Aliyu Maru

Next Post

Ba ruwa na da kamfen ɗin Tinubu, inji Rahama Sadau

Related Posts

Tawagar Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya daga Tinubu tare da yin addu’o’i a gidan Ɗantata a Madina
Nijeriya

Tawagar Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya daga Tinubu tare da yin addu’o’i a gidan Ɗantata a Madina

June 30, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta bada tabbacin akwai tsaro a Abuja duk da gargaɗin da Amurka ta ba matafiya

June 23, 2025
Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya
Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

June 21, 2025
Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa Hafsoshin Soji kan cigaban da aka samu a fannin tsaron ƙasa a shekaru biyu
Nijeriya

Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa Hafsoshin Soji kan cigaban da aka samu a fannin tsaron ƙasa a shekaru biyu

June 20, 2025
Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Next Post

Ba ruwa na da kamfen ɗin Tinubu, inji Rahama Sadau

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!