BAYAN Ƙaramar Sallah mai zuwa ne za a ƙaddamar da wani littafi mai ƙunshe da waƙoƙin fitaccen mawaƙi Aminuddeen Ladan Abubakar (Alan Waƙa) a rubuce.
Wasu manazartan Hausa ne su ka rubuta kalmomin waƙoƙin daga rerawar da ya yi, su ka fitar da littafi mai taken ‘Diwanin Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar Alan Waƙa’.
A wani saƙo da ya wallafa a Instagram, wanda mujallar Fim ta ɗauko, mawaƙin, wanda shi ne Ɗanburan Sarkin Gobir kuma Sarkin Waƙar Dutse, ya bayyana farin cikin sa kan wannan muhimmin aiki da aka yi.
Ya ce, “Mu na jaddada godiya ga Allah domin tarin ni’imomi tare da yassarewa da sahalewa ta irin wannan nasibi abin bugun gaba a raye da bayan wafati.
“Haƙiƙa wannan kundi wata manuniya ce ta sakamakon nagarta da jajircewa.
“Ashe martaba da mutunci su na daga abin nema a cikin rayuwar tauraro ba kankajere a wajen neman garin kuɗi ta kowanne hali ba.
“Sai na ke ganin abin kamar wata waibuwa irin yadda martabobi ke jeren farin ɗango kamar ana tisa ƙwayar carbi.

“Alhamdu lillahi Rabbil alamina!Babu furuci na yabo da godiya sama da wannan.
“A ƙarshe, ina miƙa godiya ga marubuta wannan littafi na ‘Diwanin Waƙoƙin Ala’, da su ka sami ikon hattama wannan kundi tun ina raye.
“Ina shaida wa masoya da manazarta cewa za a ƙaddamar da wannan littafi da ƙarfin Allah a jihar Kanon Dabo bayan Sallah da izinin Ubangijin kowa.
“Allah ya bada ikon halartar wannan gagarumin taron ƙaddamarwa da za a yi a Kano. Da zarar an saka lokaci, za a shaida maku masoya na haƙiƙa.”
A baya, an taɓa fitar da littafi mai ɗauke da waƙoƙin Ala a rubuce.
Ala dai ya na ɗaya daga cikin zaratan mawaƙan ƙasar Hausa na wannan zamanin.
Waƙoƙin sa sun zama abin nazari musamman ga ɗalibai manazarta harshen Hausa saboda yadda waƙoƙin su ke ƙunshe da hikimomin harshen Hausa.
Ya samu karramawa iri-iri saboda gudunmawar da ya ke bayarwa ga adabin Hausa.
Kafin ya fara waƙa, Ala marubucin zube ne wanda ya wallafa littattafai a kan jigon soyayya.