• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, May 15, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Za a kafa kwamitin samar da hanyoyin kai agaji a Arewa Maso Gabas

by DAGA WAKILIN MU
September 8, 2020
in Nijeriya
0
Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Kyautata Rayuwar Al'umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Kyautata Rayuwar Al'umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
Gwamnatin Tarayya za ta kafa wani kwamiti na musamman wanda zai samar da hanyoyi mafi sauƙi da za a rinƙa kai agaji ga waɗanda rikicin yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya ya shafa.
 
Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Kyautata Rayuwar Al’umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta bayyana haka a cikin wata takardar bayani ga manema labarai a Abuja ran Litinin. 
 
A cewar ta, rashin samun kaiwa ga jama’ar da rikicin ya shafa wani babban abin damuwa ne.
 
A takardar, wadda hadimar musamman kan yaɗa labarai ta ministar, Nneka Anibeze, ta rattaba wa hannu, Sadiya Farouq ta ce kula da tsaron lafiyar ma’aikatan agaji a Arewa Maso Gabas shi ma tarnaƙi ne ga aikin kai kayan agaji ga masu buƙata.
 
Ta ce: “Guruf ɗin ma’aikatan da za a naɗa za su fito da ingantacciyar hanya wadda dukkan mu za mu yi amfani da ita a matsayin ma’aikatan agaji, wanda ya haɗa da jami’an tsaro, saboda mu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da juna cikin sauƙi.
 
“Aikin mu dai na haɗin gwiwa ne, domin kowannen mu ya na buƙatar abokin aikin sa don tabbatar da aikin mu ya cika.
 
“Don haka, ma’aikatar mu ta na ƙoƙarin ta ga ta kafa wani kwamiti a matakan jihohi da na tarayya wanda zai tabbatar  da aikin ya gudana a Arewa Maso Gabas.
 
“Zai kuma haɗa gwiwa da ma’aikatu da sassan su da cibiyoyin su don ganin aikin raba agaji ya na tafiya yadda ya kamata.”
 
Ministar ta ƙara da cewa za ta tabbatar da cewa a wurin ma’aikatar ne za a samu duk wani abu da ake buƙata saboda aikin raba agaji ya tafi daidai, ciki har da kai ziyara jefi-jefi a yankin na Arewa Maso Gabas.
 
Ta ƙara da cewa ma’aikatar za ta riƙa samun rahoton wata-wata ta hannun kodineta mai kula da aikin agaji a yankin (OCHA).
 
Hajiya Sadiya ta ce za a rinƙa kai kayan abinci da wanda ba na abinci ba zuwa dukkan wuraren da abin ya shafa masu wuyar shiga idan an binciko su. 
 
“Wuraren da za a iya shiga da mota, sojoji ne za su raka mu, yayin da su kuma wuraren da ke lungu sosai za a yi amfani da jiragen Rundunar Sojin Sama ne ana cilla wa mutane kayan agajin zuwa ƙasa inda za su ɗauka.
 
“Saboda haka, dukkan mu tilas ne mu yi aiki tare da gwamnatocin jihohi, sojoji, Majalisar Ɗinkin NEMA, SEMA da ma wasu don tabbatar da cewa an kai kayan agajin ga mabuƙata.”

Loading

Previous Post

Umma Maiwaina, kakar Aminu Mirror, ta kwanta dama

Next Post

‘Yan biyu za mu aura, inji Tagwayen Asali

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
'Yan gida ɗaya masu kama ɗaya! Tagwayen Asali tare da 'yanbiyun da za su aura

'Yan biyu za mu aura, inji Tagwayen Asali

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!