• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 22, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zabiya Magajiya Ɗambatta ta rasu ta na da shekara 85

by DAGA IRO MAMMAN
October 8, 2021
in Mawaƙa
0
Marigayiya Magajiya Ɗambatta a ɗakin ta cikin sabon gidan da su Jaafar su ka gina mata. Hoto daga: Daily Nigerian

Marigayiya Magajiya Ɗambatta a ɗakin ta cikin sabon gidan da su Jaafar su ka gina mata. Hoto daga: Daily Nigerian

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAHU Akbar! Allah ya yi wa fitacciyar zabiya Magajiya Ɗambatta rasuwa, ta na da shekara 85 a duniya.

Ta rasu a yau Juma’a, 8 ga Oktoba, 2021 a garin su, wato Makoɗa da ke cikin Jihar Kano.

Magajiya ta yi fice ne a ƙarshen shekarun 1970 zuwa shekarun 1980 musamman saboda waƙar ta mai suna ‘Soriyal’ mai yin kira ga iyaye da su sanya ‘ya’ya a makaranta.

Idan kun tuna, mun taɓa ba ku labarin yadda a cikin Disamba 2019 fitaccen ɗan jaridar nan Malam Jaafar Jaafar ya jagoranci ƙaddamar da gidauniyar neman agaza wa mawaƙiyar saboda ganin halin ƙunci da ta ke ciki.

Dalili shi ne Magajiya ta makance, kuma sai ta yi bara sannan ta samu abin da za ta ci.

Jaafar, wanda shi ne Babban Editan jaridar ‘Daily Nigerian’, ya yi rubutu a lokacin da ya gano cewa Magajiya ta na raye amma ta na cikin ƙunci, ya bada labarin halin da ta ke ciki.

A rubutun, ya bayyana cewa makaɗin kalangun zabiyar, Ya’u Nakuki, da ɗan kuntukun sa sun daɗe da rasuwa, amma mawaƙiyar da wasu ‘yan amshin ta na nan da ran su.

Ya ambato rubutun da fitaccen ma’aikacin rediyo ɗin nan Alhaji Adamu Salihu ya yi a kan faifan waƙoƙin ta, inda ya ce waƙoƙin ta sun taimaka wajen saka yara makaranta da iyaye su ka riƙa yi a farkon shekarun 1970 da sama da yara 3,000 a Kano.

Jaafar ya ambato irin gudunmawar da ta bayar ga cigaban harkar ilimi, ya ce ya tabbatar wasu daga cikin yaran da iyayen su su ka sanya a makaranta a wancan lokaci yanzu sun zama farfesoshi.

Ya ce abin baƙin ciki ne a ce wadda ta yi wannan gagarumin aikin ta ƙare rayuwar ta a haka.

Sakamakon rubutun da ya yi, sai mutane su ka dinga kiran sa, su na so su bada tallafi da za a ba zabiyar.

Ganin haka, sai ɗan jaridar ya haɗa ƙarfi da wasu abokan sa guda biyu wajen gudanar da gidauniyar agaza wa Magajiya, wato Musa Abdullahi Sufi da Ibrahim Sanyi-Sanyi.

Nan da nan kuwa mutane su ka shiga tura kuɗin taimako a asusun da su Jaafar su ka buɗe, aka tara kimanin naira miliyan 5. 

Su Jaafar sun yi amfani da kuɗin wajen gina wa zabiyar gida tare da saya mata kayan abinci da yi mata tanadi na aƙalla shekara ɗaya.

Tun daga lokacin kuwa ba a ƙara jin ɗuriyar mawaƙiyar ba sai a yau da aka ji labarin rasuwar ta.

Mutane da dama sun yi baƙin cikin rasuwar Magajiya Ɗambatta tare da yi mata addu’ar samun rahama.

Allah ya rahamshe ta, amin.

Loading

Tags: Adamu SalihuDaily Nigerian newspaperIbrahim Sanyi-SanyiJaafar JaafarMagajiya ƊambattaMakodamawakan hausaMusa Abdullahi SufimutuwaYa'u Nakukizabiya
Previous Post

Furodusan Kannywood Umar UK ya yi ƙarar Hafsat Idris ya na so ta biya shi diyyar naira miliyan 10

Next Post

Tashar Africa Magic za ta shirya fim kan Aisha Buhari

Related Posts

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi
Mawaƙa

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

April 19, 2025
Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala

October 28, 2024
Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala

July 16, 2024
Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara
Mawaƙa

Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara

May 13, 2024
Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 
Mawaƙa

Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 

December 7, 2023
Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala
Mawaƙa

Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala

December 3, 2023
Next Post
Hajiya Aisha Halilu Buhari

Tashar Africa Magic za ta shirya fim kan Aisha Buhari

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!