Wanda ya rera: Abubakar Baƙin Ruwa
Wanda ya rubuta a ajami: Shu’aibu Kabuga
Farfesa Abdalla Uba Adamu ya alkin ta mana ita.
Sadiq Tukur Gwarzo ya kawo maku ita daga ajami zuwa hausar boko.
Bismillahir Rahmanir Raheem. Sallallahu Ala sayyidina Muhammad wa ahlihi wa sahbihi wa zurriyatihi wa sallim taslima.
Ta’ala Rabbuna sarkin sarauta,
Kariymu Rahiymu Allah ne da baiwa.
Idan roƙo gare ka ka roƙi Allah,
Gama shi ne ya ba wa kowa.
Sarauta da dukiya da duniya ta ba ka,
Ka bar cira kai ka na rowa ciccikawa.
Ka bar hura hanci duniya ce,
Abin da ta ba ka ba ya tabbacewa.
Ka duba sarakunan da aka yo a baya,
Da labarinu ya riƙa sai ɓacewa.
Bagauda shi ya sari Kano da fari,
Ta na daji sa’annan babu kowa.
Ya na Gaya shi Bagauda gidan sa,
Maharbi ne riƙaƙƙe mai kashewa.
Ya zo cirani ya yi bukka Maɗatai,
Ya zauna ‘yan’uwan sa su na tafowa.
Maharba gwargwado su ka ɗaura taro,
Gun sa su na kisan zaki da giwa.
Da nama ya yi yawa ɗanye ƙafaffe,
Fa ba mata maza ne ke dafawa.
Da Gwale da shi da Yakasai da Sheshe,
Da Guguwa manya-manyan Maguzawa.
Ana cewa da su su ne sarakai,
Na noma sun ka zo dawa gewayawa.
Su ka kulle dawa su ka kama gona,
Fa sai aiki iyali na tafowa.
Ga Malam Nuhu na ji babu ƙage,
Batu na ba shi tare da ƙaryatawa.
Manoman da sun ka tafo da fari,
Su kan sara su na kuma dandaɗewa.
Sa’annan sai ruwan bazara ya sauka,
Su kai shukar su ta rinƙa furfutowa.
Su kai dawa, gero ba misali,
Aka samu ana kuma ribatawa.
Su kai ƙarfi na bayi har dawaki,
Da su ne manya-manyan tajirawa.
Gabas ta taho da yamma har arewa,
Wajen kudu sun ka ɓarko Maguzawa.
Da Barnawa da Katsinawa da Daura,
Da Zamfara can ta Habi da Gobirawa.
Mutan Zurmi da su da mutan Talata,
Bakura da su Anka su na tafowa.
Su kai ta awo su na kamun gidaje,
Kabawa da Kumburawa da Adarawa.
Da tun daga Yankatsari gida ya zaga,
Ta Mariri ya kawo Gunduwawa.
Mutane na asarari sun yi shanya,
Da babu sarki fa, babu wurin tsarewa.
Da Tunbi da Sudawa shashen-ga nayza,
Su na gama kai su na kame Kanawa.
Da manya su ka ce sai an sarauta,
Su kai Sarki Bagauda mai tsarewa.