SUNAN sa John Mamman. Sunan mahaifin sa Garba Katsina. Kakannin sa sun riƙe sarautar Ƙauran Katsina kafin lokacin Jihadi.
Shi ne ɗan Arewa na farko da ya karanci ilimin tattalin arzikin ƙasa, wato ‘Economics’. Ya samu digirin sa na ‘Economics’ ne daga ƙasaitacciyar makarantar nan da ake kira ‘London School of Economics’.
Shi ne ɗan Nijeriya na farko da ya riƙe muƙamin ‘Executive Director’ a Bankin Duniya (World Bank) da ke birnin Washington, DC.
Ya na cikin ma’aikatan farko na Ma’aikatar Harkokin Ƙasashen Wajen Nijeriya tun sa’ilin da aka buɗe ta a shekarar 1950.
Shi ne ya fara buɗe ofishin jakadancin Nijeriya da ke Amurka. Ya na Amurka a lokacin da Nijeriya ta samu ‘yancin kai a ranar 1 ga Oktoba, 1960, a nan su ka yi walimar murnar samun ‘yanci.
John Mamman Garba ya riƙe muƙamin Ambasadan Nijeriya a ƙasashe biyar – Amurka da Italiya da Girka da Cyprus da Andalus (Spain).
Kamar yadda mu ka sha faɗi mu na nanatawa, a ƙasar nan kullum so ake a nuna Bahaushe bai isa ba. Duk inda Bahaushe ya yi fice, ko dai a kore masa hausancin sa ko a naƙasa asalin sa ko kuwa a yi ƙoƙarin binne tarihin sa.
An yi ƙoƙarin binne tarihin Ambasada John Mamman Garba.

Ba titi ko layi ko gini ko cibiyar nazari ko ɗakin karatu da sauran su da aka sanya wa sunan sa don tunawa da shi.
Mun san mafi yawancin masu karatun wannan rubutun sai yanzu su ka fara jin sunan wannan bawan Allah.
Amma Allah cikin ikon sa, ya ba Ambasada Mamman Garba damar rubuta tarihin rayuwar sa da kan sa cikin wani littafi mai shafi kusan 400 da ya sa wa suna ‘The Time Has Come…’, wanda kamfanin wallafa littattafai na Spectrum ya buga.
Ambasada Mamman Garba ya koma ga mahaliccin sa a shekarar 1989 kafin littafin da ya rubuta ya fito daga ɗab’i, ya na da shekaru 70 a duniya. Akwai ‘ya’ya da jikokin sa a Wusasa ta Zariya inda ya yi rayuwar sa.
Mu na alfahari da Ambasada John Mamman Garba.
© Nigerian Bahaushe