• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, June 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

2023: INEC ta ƙayyade wa jam’iyyu wa’adin kammala zaɓuɓɓukan fidda gwani

by DAGA ALI KANO
May 7, 2022
in Nijeriya
0
Mista Festus Okoye

Mista Festus Okoye

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gargaɗi jam’iyyun siyasa da su tabbatar da cewa sun kiyaye jadawalin gudanar da zaɓuɓɓukan su na fidda gwani na manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023.

Babban Kwamishina kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da kan Masu Zaɓe na hukumar, Mista Festus Okoye, shi ne ya bada wannan gargaɗin cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

Okoye ya tunatar da cewa a ranar 26 ga Fabrairu, 2022, hukumar ta fitar da Jadawali da Tsarin Ayyuka na Manyan Zaɓuɓɓukan 2023, inda ta tanadar wa jam’iyyun da cewar su gudanar da zaɓuɓɓukan fidda gwanayen su don tsaida ‘yan takara daga ranar 4 ga Afrilu zuwa 3 ga Yuni, 2022.

Wannan na nufin cewa hukumar ba za ta amince da duk wani zaɓen fidda gwani da aka yi bayan wa’adin ya cika ba.

Kwamishinan ya ce: “Domin kiyaye sashe na 82(1) na Dokar Zaɓe ta 2022, dukkan jam’iyyun siyasa 18 sun bada sanarwar da ake buƙata da ke nuna ranakun da za su yi manyan tarurrukan su na ƙasa, da zaɓuɓɓukan fidda gwani domin tsayar da ‘yan takarar muƙamai daban-daban kamar yadda aka zayyana a Tsarin Mulki da Dokar Zaɓe.

“Wasu daga cikin jam’iyyun har sun fara aikin, wanda ya sa hukumar ta tura ma’aikata domin su sa ido kan yadda ake ayyukan kamar yadda doka ta buƙace ta ta yi.

“Saboda ganin muhimmancin aikin wajen samar da ‘yan takarar muƙamai daban-daban na zaɓe a Manyan Zaɓuɓɓukan 2023, ya na da muhimmanci a tunatar da jam’iyyun siyasa cewa ya rage masu wata ɗaya daga yau su kammala zaɓuɓɓukan su na fidda gwani.

“Wa’adin ƙarshe dai shi ne ranar Juma’a, 3 ga Yuni, 2022. Yayin da ta ke kira ga jam’iyyun da su tabbatar da sun yi zaɓe babu wata hatsaniya, kuma fisabillahi, hukumar ta na nanata cewa wa’adin na nan daram daƙam babu canzawa.” 

Okoye ya kuma ce ana so a miƙa sunayen ‘yan takarar zaɓen Shugaban Ƙasa da Majalisar Tarayya ne ta hanyar gidan yanar INEC daga ranar 10 zuwa 17 ga Yuni, yayin da za a miƙa sunayen ‘yan takarar gwamna da majalisun dokokin jihohi daga ranar 1 zuwa 15 ga Yuli.

“Ana ƙara tunatar da jam’iyyun siyasa cewa tilas ne sunayen ‘yan takarar da za su  miƙa wa hukumar su kasance waɗanda aka samar ne ta hanyar zaɓen fidda gwani da aka yi fisabilillahi.”

Okoye ya ce hukumar za ta ci gaba da yin aiki tare da jam’iyyun siyasar don tabbatar da an kiyaye Tsarin Mulki da Dokar Zaɓe da jadawalin dukkan ayyukan da aka tsara yi a cikin Jadawali da Tsarin Ayyukan Manyan Zaɓuɓɓukan 2023.

Loading

Tags: Dokar ZaɓeElectoral ActFarfesa Mahmood YakubuFestus OkoyeINECjadawalijam'iyyuTsarin Mulkizaɓuɓɓukan 2023
Previous Post

Adabin Bariki

Next Post

An yi tir da masu cewa shugaban INEC ya fito takarar shugaban ƙasa

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

An yi tir da masu cewa shugaban INEC ya fito takarar shugaban ƙasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!