• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

2023: INEC ta ƙayyade wa jam’iyyu wa’adin kammala zaɓuɓɓukan fidda gwani

by DAGA ALI KANO
May 7, 2022
in Nijeriya
0
Mista Festus Okoye

Mista Festus Okoye

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gargaɗi jam’iyyun siyasa da su tabbatar da cewa sun kiyaye jadawalin gudanar da zaɓuɓɓukan su na fidda gwani na manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023.

Babban Kwamishina kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da kan Masu Zaɓe na hukumar, Mista Festus Okoye, shi ne ya bada wannan gargaɗin cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

Okoye ya tunatar da cewa a ranar 26 ga Fabrairu, 2022, hukumar ta fitar da Jadawali da Tsarin Ayyuka na Manyan Zaɓuɓɓukan 2023, inda ta tanadar wa jam’iyyun da cewar su gudanar da zaɓuɓɓukan fidda gwanayen su don tsaida ‘yan takara daga ranar 4 ga Afrilu zuwa 3 ga Yuni, 2022.

Wannan na nufin cewa hukumar ba za ta amince da duk wani zaɓen fidda gwani da aka yi bayan wa’adin ya cika ba.

Kwamishinan ya ce: “Domin kiyaye sashe na 82(1) na Dokar Zaɓe ta 2022, dukkan jam’iyyun siyasa 18 sun bada sanarwar da ake buƙata da ke nuna ranakun da za su yi manyan tarurrukan su na ƙasa, da zaɓuɓɓukan fidda gwani domin tsayar da ‘yan takarar muƙamai daban-daban kamar yadda aka zayyana a Tsarin Mulki da Dokar Zaɓe.

“Wasu daga cikin jam’iyyun har sun fara aikin, wanda ya sa hukumar ta tura ma’aikata domin su sa ido kan yadda ake ayyukan kamar yadda doka ta buƙace ta ta yi.

“Saboda ganin muhimmancin aikin wajen samar da ‘yan takarar muƙamai daban-daban na zaɓe a Manyan Zaɓuɓɓukan 2023, ya na da muhimmanci a tunatar da jam’iyyun siyasa cewa ya rage masu wata ɗaya daga yau su kammala zaɓuɓɓukan su na fidda gwani.

“Wa’adin ƙarshe dai shi ne ranar Juma’a, 3 ga Yuni, 2022. Yayin da ta ke kira ga jam’iyyun da su tabbatar da sun yi zaɓe babu wata hatsaniya, kuma fisabillahi, hukumar ta na nanata cewa wa’adin na nan daram daƙam babu canzawa.” 

Okoye ya kuma ce ana so a miƙa sunayen ‘yan takarar zaɓen Shugaban Ƙasa da Majalisar Tarayya ne ta hanyar gidan yanar INEC daga ranar 10 zuwa 17 ga Yuni, yayin da za a miƙa sunayen ‘yan takarar gwamna da majalisun dokokin jihohi daga ranar 1 zuwa 15 ga Yuli.

“Ana ƙara tunatar da jam’iyyun siyasa cewa tilas ne sunayen ‘yan takarar da za su  miƙa wa hukumar su kasance waɗanda aka samar ne ta hanyar zaɓen fidda gwani da aka yi fisabilillahi.”

Okoye ya ce hukumar za ta ci gaba da yin aiki tare da jam’iyyun siyasar don tabbatar da an kiyaye Tsarin Mulki da Dokar Zaɓe da jadawalin dukkan ayyukan da aka tsara yi a cikin Jadawali da Tsarin Ayyukan Manyan Zaɓuɓɓukan 2023.

Loading

Tags: Dokar ZaɓeElectoral ActFarfesa Mahmood YakubuFestus OkoyeINECjadawalijam'iyyuTsarin Mulkizaɓuɓɓukan 2023
Previous Post

Adabin Bariki

Next Post

An yi tir da masu cewa shugaban INEC ya fito takarar shugaban ƙasa

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

An yi tir da masu cewa shugaban INEC ya fito takarar shugaban ƙasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!