• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 23, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gidan yanar kallon finafinan Hausa, Kallo.ng, ya samu karramawa ta duniya

by DAGA ALI KANO
July 31, 2022
in Labarai
0
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GIDAN yanar nan mai watsa wa ‘yan kallo finafinan Hausa ta hanyar intanet, wato Kallo.ng, ya samu kyautar karramawa ta duniya, watanni takwas kacal bayan an ƙaddamar da shi.

Ya samu kyautar sabon gidan yanar watsa shirye-shirye da fi kowanne iya ƙirƙira, wato ‘Best New Streaming Innovation’, daga kamfanin Marketing World Awards (MWA), a taron shekara-shekara na 11 da ya gudanar a Ankara, babban birnin ƙasar Ghana, a ranar 15 ga Yuli, 2022.

Manajar Darakta kuma mamallakiyar kamfanin gidan yanar, Hajiya Maijidda Modibbo, ta bayyana farin cikin ta kan wannan karramawar wadda ta kira da “babbar nasara.”

A sanarwar da ta bayar a ranar Asabar, Maijidda ta ce ta samu wannan karramawar ne sakamakon aiki tuƙuru da ta ke yi da kuma hazaƙar ƙirƙira wadda ta sa ingancin gidan yanar ya yi daidai da yadda ake buƙatar sa a ko’ina a duniya.

A cewar ta, Kallo.ng ya yi nisa wajen amfani da dabarun fasaha na zamani domin ya zama mai tasiri kuma mai jan hankali, ba domin komai ba sai saboda ya biya wa masu son kallon finafinan Hausa buƙata.

Ta bayyana cewa a cikin watanni takwas da ya yi, gidan yanar kallo.ng ya samu sama da mutum 35,000 da su ka yi rajista su na amfani da shi, sannan yawan su zai ƙaru nan ba da daɗewa ba saboda ana samun ƙarin masu kallo da ke kallon finafinai ta hanyar gidan yanar.

Maijidda ta ce: “Wannan karramawa tukwici ne na aiki tuƙuru da mu ke yi domin biya wa abokan cinikayyar mu buƙata. Ƙungiyar da ta ba mu karramawar ƙungiya ce da aka san da ita kuma ake girmama ta a duniya. 

“Karramawar, wadda mu ka samu bayan watanni shida kacal da ƙaddamar da gidan yanar, ba za ta sa mu shagala ba, a maimakon hakan sai ma ta ƙara mana ƙarfin hali domin mu biya wa abokan hulɗar mu buƙata kuma mu tafi daidai da ƙasashen da su ka ci gaba.”

Shugabar ta kuma faɗa wa waɗanda su ka yi rajista da gidan yanar da duk wani mai son finafinan Hausa cewa su sa ido su ga ƙarin abubuwan burgewa da cigaban da za ta kawo, waɗanda manufar su ita ce a ƙara inganta gidan yanar don ya tafi daidai da na ƙasashen da su ka ci gaba.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa kamfanin Spacekraft Media Limited ne ya kafa Kallo.ng a cikin watan Nuwamba, 2021.

Loading

Tags: AccraAnkarafilm streamingfinafinan hausaGhanahausa filmsintanetkallo.ngKannywoodMaijiddaMaijidda ModibboMarketing World AwardsSpacekraft Media Limited
Previous Post

Kidinafas sun nemi a biya diyyar dala 100,000 kafin su sako jaruman fim biyu

Next Post

Cewar Hadiza Gabon a kotu: Rayuwa ta ta na cikin haɗari

Related Posts

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Next Post
Hadiza Aliyu Gabon

Cewar Hadiza Gabon a kotu: Rayuwa ta ta na cikin haɗari

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!