MAWAƘI kuma jarumi a Kannywood, Alhaji Aliyu Ibrahim, wanda aka fi sani da Aliyu Haidar ko Hambal a cikin shirin ‘Labari Na’, ya bayyana irin farin cikin da ya tsinci kan sa a ciki lokacin da Sarkin Kalshingi ya naɗa shi sarautar Ɗan Adalan Kalshingi.
Aliyu Haidar ya yi bayanin hakan ne a lokacin da ya ke zantawa da mujallar Fim kwanan nan a Kaduna.
Ɗan Adalan na Kalshingi ya ce, “Na ji daɗi matuƙa, kuma na yi murna. Saboda ni wannan bawan Allah, Mai Martaba Sarki Hussaini Abubakar Magaji, ya yi min abin da ba zan iya mantawa a duniya ba. Bai san ni ba, bai taɓa gani na ba, bai taɓa mu’amala da ni ba, amma kasancewar jin yadda na ke kyautata wa al’umma in ina da shi da kuma irin tausaya wa al’umma da na ke yi in ina da shi, kuma da ya kalle ni a fim ɗin ‘Labari Na’, sai ya ce kai wannan ya burge ni, gaskiya dole in jawo wannan ya zama a matsayin ɗan fada na.
“Wallahi da aka turo min takardar naɗi na Ɗan Adalan Kalshingi, wallahi na ji daɗi ɗari bisa ɗari. Kuma in-sha Allahu za mu gayyace ku, za ku zo taron naɗi “
Idan ba ku manta ba, a ranar Litinin, 5 ga Disamba, 2022, mujallar Fim ta ba da labarin cewa Mai Martaba Sarkin Kalshingi da ke cikin Ƙaramar Hukumar Yamaltu/Deba a Jihar Gombe ya ba Ali Haidar sarautar Ɗan Adalan Kalshingi.