Bikin auren diyar Shugaban Kasa, Zahra Buhari, da mijin ta Ahmed Indimi da ya gudana a cikin watan jiya biki ne da ya dauki hankalin mutane a ciki da wajen kasar nan. Ya kasance abin tattaunawa a duk wajen taruwar jama’a da ma wadanda su ke kan hanya su na tafiya.
Kamar yadda bikin ya ja hankalin mutane, haka ma zuwan fitacciyar mawakiya Fati Nijar ya dauki hankalin mutane domin ita kadai ce mace da ta halarci bikin a duk mawakan Kannywood. Wannan ya kara fito da matsayi da kuma shaharar da Fati ta ke da shi a cikin abokan sana’ar ta.
Baya ga haka, ko a wajen bikin da aka yi a fadar shugaban kasa a Abuja, Fati Nijar ta zama kallabi tsakanin rawuna, domin kuwa akwai mawaka maza da dama na Kannywood da su ka halarci bikin, amma duk ba a san da zuwan su ba. Yawancin su sun tashi a matsayin ’yan kallo ne, don kuwa har su ka je su ka dawo ba a san da zuwan su ba; duk da yadda aka yada hotunan bikin a duniya, sam ba a nuno hotunan su ba. Hotunan Fati kadai aka yada a duniya ta na zuba waka.

Fati Nijar (Gimbiyar Mawakan Borgu) ta shaida wa wakilin mu cewa ta halarci bikin ne don ta yi waka a ranar Kamun Amarya, amma sai abin ya zame mata biyu, don kafin a yi kamun sai Uwargidan Shugaban Kasa, Hajiya A’isha Muhammadu Buhari, ta shirya wani zama na musamman wanda ba kowace mace za ta halarci wajen ba sai matan gwamnoni da ministoci da wasu kasaitattun matan kadai, to kuma sai aka kira Fati don ta zama zabiyar wajen daga ita sai manyan baki, aka ba ta lokaci ta yi sharafin ta, aka sha rawa ba irin ta gala ba.
A ranar Kamu ma dai Fatin ce ta yi zarra a cikin mawaka, saboda ko a nan ma ita ta ce dauke hankalin mahalarta bikin cikin wakokin ta masu kayatarwa, don haka ba abin mamaki ba ne da mutane su ke cewa idan ban da amarya da ango, to babu wani mutum da ya dauki hankalin mutane kamar Fati Nijar.

Da mu ka tambaye ta yadda ta ji a wajen wannan biki, cewa ta yi, “A gaskiya wannan abin ina alfahari da shi kuma ina kara yi wa Allah godiya. Domin kuwa abin alfahari ne a gare ni kasancewa ta a wajen wannan biki. Duk da na sha halartar wajen bukukuwa da yawa ina yin waka, amma dai ba kamar wannan ba. A ce an gayyace ka bikin ’yar Shugaban Kasa, ka je ka zama mai waka a wajen ai ka ga abin alfahari ne. Ni na san ba iyawa ta ba ce, daukaka ce daga Allah, kuma ina kara godiya a gare Shi bisa ni’imar ya yi mini. Ina rokon Sa kuma Ya kara mini basira da godiya a gare Shi.”
Daga karshe, Fati Nijar ta yi fatan Allah Ya kara hada kan mawaka, Ya daukaka sana’ar su.
To, amin.