• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ministan Yaɗa Labarai ya ƙaddamar da ginin Radio House da aka gyara, tare da alƙawarin ƙarin gyare-gyare

by Editors
December 18, 2024
in Nijeriya
0
Ministan Yaɗa Labarai ya ƙaddamar da ginin Radio House da aka gyara, tare da alƙawarin ƙarin gyare-gyare

Minista Idris yana yanka zare don ƙaddamar da gyararren ginin Radio House a Abuja a yau Laraba

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da ginin Radio House da aka gyara a Abuja, wanda ke nuna wani babban mataki na dawo da muhimman ababen more rayuwa da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.

Da yake zagaye don duba ginin mai hawa 14, ministan ya bayyana halin lalacewar da ginin ya shiga har tsawon kusan shekaru 20.

Ya ce: “Lokacin da na zo nan, wurin nan ya lalace— na’urorin esi ba sa aiki, lif na hawa ba ya aiki, kuma ma’aikata na hawa har hawa tara ko goma don isa ofisoshin su. Hatta banɗakuna sun lalace; wannan bai dace ba.”

Ministan ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa gaggawar amincewar da ya yi na kuɗaɗen da suka ba da damar gyaran ginin, wanda ke ɗauke da ma’aikatar da kuma Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya.

Minista a cikin ofishin sa

“Bisa taimakon Shugaban Ƙasa, mun mayar da wannan ginin ya zama wurin aiki mai amfani kuma mai inganci, na’urorin esi suna aiki, dukkan lif suna aiki, kuma kayan aikin sun zama na zamani. A karo na farko cikin kusan shekaru ashirin, Radio House ya dawo aiki, kuma ma’aikata suna farin ciki.”

A cewar Dakta Suleiman Haruna, Daraktan Hulɗa da Jama’a da Tsare-tsare, wannan aikin ya dace da burin Shugaba Tinubu na zamanantar da ababen more rayuwa na aikin yaɗa labarai a duk faɗin ƙasar nan.

Ministan ya jaddada cewa ana ci gaba da ƙoƙarin yin irin wannan gyaran a tashoshin Rediyon Tarayya na Nijeriya (FRCN) da Gidan Talabijin na Nijeriya (NTA) da ke Kaduna, Legas, da Inugu.

Ya ce: “Muna dawo da darajar kadarorin yaɗa labarai na Nijeriya kamar yadda suke a da. Wannan ba kawai gyaran gine-gine ba ne; yana nufin mayar da masana’antar kafofin watsa labarai na Nijeriya ta dace da mafi kyawun masana’antu a duniya.”

Ministan ya kuma yi kira ga ma’aikatan da su yi amfani da wannan tagomashin da gwamnati ta bayar ta hanyar yin aiki da ƙwazo da ƙwarewa.

Ya ƙara da cewa, “Yanzu da ake ba mu abubuwa masu yawa, dole ne mu ma mu mayar da martani ta hanyar tallafa wa burin Shugaban Ƙasa na farfaɗo da martabar Nijeriya.”

Ya jaddada muhimmancin ƙwararrun ‘yan jarida wajen bunƙasar ƙasa, tare da alƙawarin kare yanayin aiki mai kyau, wanda ya haɗa da samar da tsarin albashi da ya dace da matsayin su.

Idris ya ce: “Shugaban Ƙasa yana ƙoƙarin yin duk mai yiwuwa don kula da dukkan ɓangarori, amma saboda rawar da kafofin watsa labarai suke takawa da kuma haɗarin da ke tattare da aikin, muna fatan ganin ‘yan jarida suna samun tsarin albashi da ya dace da irin aikin da suke yi wa ƙasar mu.”

Minista Idris yana karɓar kambin karramawa daga Shugabar ƙungiyar ma’aikatan Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Kwamared Chika Ukachukwu a lokacin taron ƙaddamar da gyararren ginin Radio House

A nata ɓangaren, Shugabar Kwamitin Haɗin Gwiwa na Ma’aikata a ma’aikatar, Kwamared Chika Ukachukwu, ta yaba da aikin gyaran da aka yi, tana mai cewa kyakkyawan yanayin aiki da aka yi zai ƙarfafa wa ma’aikata gwiwa.

Ta kuma miƙa kyautar Gwarzon Jagoranci ga ministan a matsayin yabo bisa jajircewar sa da sadaukarwar sa wajen cimma burin ma’aikatar.

Taron ya samu halartar Muƙaddashin Babbar Sakataren Ma’aikatar, Comfort Ajiboye, da Darakta Janar na FRCN, Alhaji Muhammad Bulama.

Loading

Tags: gyaran giniMohammed IdrisRadio House
Previous Post

Za a ƙarfafa gyare-gyaren tsarin tattalin arziki da Tinubu ke yi a 2025, inji Ministan Yaɗa Labarai

Next Post

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

'Dakan ɗaka...': Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!