• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 18, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Kano za ta ɗauki nauyin taron ƙasa kan haɓaka masana’antar fasaha 

by IRO MAMMAN
June 17, 2025
in Labarai
0
Gwamna Abba Kabir Yusuf

Injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta amince za ta ɗauki nauyin babban taron ƙasa da za a yi kan hanyoyin haɓaka masana’antar fasaha domin inganta tattalin arzikin Nijeriya.

Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Kwamared Ibrahim Waiya, shi ne ya faɗi haka a cikin wata takarda ga manema labarai da ya saki a yau, inda ya ce amincewar ta biyo bayan gamsuwar da ta yi da takardar neman buƙatar hakan wadda ƙungiyar Kannywood Foundation ta miƙa mata.

Gwamnatin ta yi la’akari da yadda ƙungiyar, a takardar tata, ta nuna muhimmiyar rawar da Kano ke takawa a matsayin ta na cibiyar ayyukan al’adu da fasaha a Arewacin Nijeriya.

Kwamishinan ya ce: “Babban taron zai kasance wani muhimmin waje inda za a baje kolin ɗimbin albarkatun da Kano take da su a industirin fasaha, wadda ta haɗa da harkar shirya finafinai, kayan kwalliya, sana’o’in hannu, kaɗe-kaɗe da waƙe-waƙe, rubutu, da ƙirƙirar saƙonnin intanet.

“Ana sa ran babban taron zai jawo muhimman masu ruwa da tsaki daga sassa daba-daban na ƙasar nan, waɗanda suka haɗa da hukumomin cigaban al’umma na ƙasa da ƙasa, ma’aikatun da hukumomin gwamnatin tarayya, ‘yan kasuwar fasaha, masu zuba jari, da kamfanonin manhajojin intanet irin su Netflix da Amazon.

“Abubuwan da za a tattauna a taron za su kasance ne kan yadda za a yi amfani da ɓangaren fasaha wajen faɗaɗa tsarin tattalin arziki, da samar da aikin yi, da bunƙasa ƙirƙira a cikin al’umma.

“Domin tabbatar da ingantaccen tsari da aiwatar da taron, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma amince da kafa Kwamitin Shirya Taro (LOC), wanda zai ƙunshi manyan masu ruwa da tsaki daga ita gwamnatin, da ɓangaren ‘yan kasuwa, da ƙungiyoyin masana’antar fasaha, da sarakuna gargajiya da kuma manyan makarantu.

“Taron ba kawai taron je ka na yi ka ba ne, sabon abu ne da za a yi amfani da shi wajen aza Jihar Kano State a kan gaban tsarin tattalin arzikin fasaha na Nijeriya.

“Kannywood, wato masana’antar mu ta finafinai, tare da sanannun masu sana’o’in hannu da muke da su, waɗanda an san su a duniya, suna ci gaba da samun ficen da ya dace. Ta hanyar wannan babban taron, Kano na fatan ta samar da haɓakar tattalin arziki mai ɗorewa, ta rungumi matasan mu, kuma ta buɗe sabbin ƙofofin wasu damarmarkin cigaba wanda ya yi daidai da hangen nesa tare da kishin jama’a irin na Gwamna Abba Kabir Yusuf.”

Gwamnatin ta yi kira ga dukkanin masu ruwa da tsaki da su bada goyon bayan su da sadaukarwa domin a cimma nasara a wannan abu na tarihi wanda ya dace da manyan muradan wannan gwamnati na ganin an ƙarfafa rayuwar matasa, an faɗaɗa hanyoyin tattalin arziki, kuma an inganta tare da farfaɗo da al’adu.”

Loading

Previous Post

Tsohon Ministan Shari’a, Malami ya jajanta wa Adam Zango kan haɗarin mota da ya yi 

Related Posts

Tsohon Ministan Shari’a, Malami ya jajanta wa Adam Zango kan haɗarin mota da ya yi 
Labarai

Tsohon Ministan Shari’a, Malami ya jajanta wa Adam Zango kan haɗarin mota da ya yi 

June 17, 2025
AFMAN ta taya Sarari murnar samun damar halartar taron baje-kolin finafinan Nijeriya a Toronto da fim ɗin ‘Kakanda’
Labarai

AFMAN ta taya Sarari murnar samun damar halartar taron baje-kolin finafinan Nijeriya a Toronto da fim ɗin ‘Kakanda’

June 16, 2025
Naɗa ni jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry Powder da aka yi zai amfani Kannywood baki ɗaya, inji furodusa Abubakar Galadima
Labarai

Naɗa ni jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry Powder da aka yi zai amfani Kannywood baki ɗaya, inji furodusa Abubakar Galadima

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!