• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Kano za ta ɗauki nauyin taron ƙasa kan haɓaka masana’antar fasaha 

by IRO MAMMAN
June 17, 2025
in Labarai
0
Gwamna Abba Kabir Yusuf

Injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta amince za ta ɗauki nauyin babban taron ƙasa da za a yi kan hanyoyin haɓaka masana’antar fasaha domin inganta tattalin arzikin Nijeriya.

Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Kwamared Ibrahim Waiya, shi ne ya faɗi haka a cikin wata takarda ga manema labarai da ya saki a yau, inda ya ce amincewar ta biyo bayan gamsuwar da ta yi da takardar neman buƙatar hakan wadda ƙungiyar Kannywood Foundation ta miƙa mata.

Gwamnatin ta yi la’akari da yadda ƙungiyar, a takardar tata, ta nuna muhimmiyar rawar da Kano ke takawa a matsayin ta na cibiyar ayyukan al’adu da fasaha a Arewacin Nijeriya.

Kwamishinan ya ce: “Babban taron zai kasance wani muhimmin waje inda za a baje kolin ɗimbin albarkatun da Kano take da su a industirin fasaha, wadda ta haɗa da harkar shirya finafinai, kayan kwalliya, sana’o’in hannu, kaɗe-kaɗe da waƙe-waƙe, rubutu, da ƙirƙirar saƙonnin intanet.

“Ana sa ran babban taron zai jawo muhimman masu ruwa da tsaki daga sassa daba-daban na ƙasar nan, waɗanda suka haɗa da hukumomin cigaban al’umma na ƙasa da ƙasa, ma’aikatun da hukumomin gwamnatin tarayya, ‘yan kasuwar fasaha, masu zuba jari, da kamfanonin manhajojin intanet irin su Netflix da Amazon.

“Abubuwan da za a tattauna a taron za su kasance ne kan yadda za a yi amfani da ɓangaren fasaha wajen faɗaɗa tsarin tattalin arziki, da samar da aikin yi, da bunƙasa ƙirƙira a cikin al’umma.

“Domin tabbatar da ingantaccen tsari da aiwatar da taron, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma amince da kafa Kwamitin Shirya Taro (LOC), wanda zai ƙunshi manyan masu ruwa da tsaki daga ita gwamnatin, da ɓangaren ‘yan kasuwa, da ƙungiyoyin masana’antar fasaha, da sarakuna gargajiya da kuma manyan makarantu.

“Taron ba kawai taron je ka na yi ka ba ne, sabon abu ne da za a yi amfani da shi wajen aza Jihar Kano State a kan gaban tsarin tattalin arzikin fasaha na Nijeriya.

“Kannywood, wato masana’antar mu ta finafinai, tare da sanannun masu sana’o’in hannu da muke da su, waɗanda an san su a duniya, suna ci gaba da samun ficen da ya dace. Ta hanyar wannan babban taron, Kano na fatan ta samar da haɓakar tattalin arziki mai ɗorewa, ta rungumi matasan mu, kuma ta buɗe sabbin ƙofofin wasu damarmarkin cigaba wanda ya yi daidai da hangen nesa tare da kishin jama’a irin na Gwamna Abba Kabir Yusuf.”

Gwamnatin ta yi kira ga dukkanin masu ruwa da tsaki da su bada goyon bayan su da sadaukarwa domin a cimma nasara a wannan abu na tarihi wanda ya dace da manyan muradan wannan gwamnati na ganin an ƙarfafa rayuwar matasa, an faɗaɗa hanyoyin tattalin arziki, kuma an inganta tare da farfaɗo da al’adu.”

Loading

Previous Post

Tsohon Ministan Shari’a, Malami ya jajanta wa Adam Zango kan haɗarin mota da ya yi 

Next Post

Mahaifiyar Sani Maikatanga, tsohon editan mujallar Fim, ta rasu

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Mahaifiyar Sani Maikatanga, tsohon editan mujallar Fim, ta rasu

Mahaifiyar Sani Maikatanga, tsohon editan mujallar Fim, ta rasu

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!