• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cutar korona: ‘Yan Nijeriya 198 sun dawo daga Lebanon – Sadiya Farouq

by DAGA WAKILIN MU
August 14, 2020
in Nijeriya
0
Wasu 'yanmata 'yan Nijeriya da aka yi fataucin su

Wasu 'yanmata 'yan Nijeriya da aka yi fataucin su

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
MINISTAR Harkokin Agaji Da Jinƙai, Hajiya Sadiya Farouq, ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya 198, waɗanda su ka maƙale a ƙasar Lebanon sakamakon hutun dole na annobar korona, yanzu sun samu damar dawowa gida. 
 
A cewar ministar, ma’aikatar ta, tare da haɗin gwiwar Cibiyar Yaƙi Da Fataucin Mutane ta Ƙasa (NAPTIP) da kuma Cibiyar Agajin Gaugawa ta Ƙasa (NEMA), sun tarbi waɗanda su ka dawo ɗin a ranar Laraba, 12 ga Agusta da ranar Alhamis, 13 ga Agusta, 2020. 
 
A wata sanarwa ga manema labarai da aka bayar a ranar Juma’a, ministar ta kuma bayyana cewa akwai ‘yanmata ‘yan Nijeriya 5,000 da su ke maƙale a Lebanon yanzu.
 
Ta ce, “Jimillar ‘yan Nijeriya 198 waɗanda su ka maƙale a Lebanon sun samu ‘yancin su kuma sun iso gida.
 
‘’Akwai aƙalla ‘yanmata ‘yan Nijeriya 5,000 a maƙale a Lebanon bayan an ja su an kai su da sunan wai za su yi aikatau a gidaje, wanda daga cikin su Ofishin Jakadancin Nijeriya ya kammala tattara bayanai kan mutum 256 waɗanda su ka amince su dawo gida.
 
“Ma’aikatar mu tare da cibiyoyin da abin ya shafa a ƙarƙashin ta sun sadaukar da kan su wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriyan da su ka maƙale a Lebanon da wasu ƙasashen sun dawo gida lafiya lau.”
 
Hajiya Sadiya ta ƙara da cewa gwamnati ta samu kiraye-kirayen neman agaji daga ‘yanmata ‘yan Nijeriya a Saudi Arebiya, Oman, Masar da sauran sassan ƙasashen ƙasashen yankin Gabas ta Tsakiya.
 
Saboda haka ta yi kira ga ‘yan Nijeriya, musamman matasa, da su guji  bari ana yaudarar su ta hanyar shafa masu mai a baki da alƙawuran ƙarya cewa za su samu rayuwa mafi inganci a can, nan kuwa aikin zubar da mutunci za su je yi.
 
Maimakon haka, ta shawarce su da su yi amfani da shirye-shirye daban-daban da ke akwai waɗanda gwamnati ta fito da su domin taimaka masu su samu hanyoyin kyautata rayuwar su a cikin Nijeriya. 
 
Ta ƙara da cewa babu inda ya fi gida.
 
Ministar ta yaba da aikin masu ruwa da tsaki cikin lamarin irin su gwamnatin Jihar Oyo, da IOM da al’ummar ‘yan ƙasar Lebanon da ke Nijeriya saboda goyon bayan da su ka bayar wajen dawo da ‘yan Nijeriyar gida lafiya lau.
 
Ta nanata cewa za a ɗauki bayanan dukkan waɗanda su ka dawo ɗin tare da goyon bayan hukumar NAPTIP.
 

Loading

Previous Post

Gwamnati za ta kafa Cibiyar Dattawa ta Ƙasa

Next Post

INEC ta ƙaddamar da sabon Tsarin Sadarwa

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

INEC ta ƙaddamar da sabon Tsarin Sadarwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!