• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 8, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Amarya Sa’a Vocal: Aure ba zai hana ni rubutu ba

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
December 13, 2020
in Labarai
0
Sa'adatu Isah Muhammad (Sa'a Vocal)

Sa'adatu Isah Muhammad (Sa'a Vocal)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
FITACCIYAR mawaƙiya kuma marubuciya, Sa’adatu Isah Muhammad (wadda aka fi sani da laƙabin Sa’a Vocal) ta bayyana cewa aure da za ta yi a ranar Lahadi mai zuwa ba zai hana ta ci gaba da rubutu ba, sai ma abin da ya yi gaba. 
 
Sa’a Vocal ta bayyana hakan ne yayin tattaunawar ta da mujallar Fim kan batun auren ta da za a ɗaura a ranar 20 ga Disamba, 2020.
 
Sa’a matashiyar marubuciyar labaran hikaya na zube ce kuma sananniyar mawaƙiya a masana’antar finafinan Hausa.
 
Haka kuma ma’aikaciya ce a gidan talbijin na Arewa24 da ke Kano.
 
‘Yar asalin Kano, Sa’a Vocal ta na aikin waƙa ne yawanci tare da fitaccen mawaƙi Naziru M. Ahmad (Sarkin Waƙa). 
 
Ɗimbin waƙokin da ta yi tare sun haɗa da ‘Mai Waƙa’, ‘Ba Zan Sake Ki Ba’, ‘Mati Da Lado’ da kuma ‘Mati a Zazzau’.
 
Haka kuma ta yi waƙa da Nazifi Asnanic mai suna ‘Ƙasar Mu Najeriya’, da dai sauran mawaƙa. 
 
A ɓangaren rubutu kuma, Sa’a Vocal ta rubuta littattafai da su ka haɗa da ‘Ƙauna Ce Sila’ da ‘Ƙaddarar Mu’. 
 
Mujallar Fim ta tambayi mawaƙiyar idan angon nata shi ma mawaƙi ne ko wani jarumi a Kannywood, sai ta amsa da cewa, “Ba ɗaya; ma’ana ba daga cikin mawaƙa ya ke ba, kuma ba daga cikin jarumai ya ke ba.” Ta ƙara da cewa, “Kawai dai Allah ne ya hukunta hakan.” 
Katin gayyatar auren Sa’a Vocal
 
 
A kan batun yadda zaman aure zai shafi rubutun ta da sana’ar ta ta waƙa, amaryar ta bayyana cewa, “Ko bayan yin aure na ina sa ran zan ci gaba da yin ayyuka na na rubututtuka, wanda kuma ina da yaƙinin cewa rubutun za su faɗaɗa fiye da yadda na ke yi da. Waƙa kuma a yanzu ba zan iya cewa komai a kan ta ba.”
 
A ƙarshe, Sa’a Vocal ta gode wa masoyan ta, marubuta, mawaƙa, ‘yan Arewa24 da kuma ogan ta Naziru M. Ahmad.
 
Ta kuma buƙaci masoyan ta da su taya ta da addu’a, ta na fatan idan sun tuna ta za su yi mata addu’ar dacewa a duk rayuwar da ta tsinci kan ta.
 
Za dai a ɗaura auren Sa’adatu Isah da angon ta Haiwatu Sa’id Daud a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 11:00 na safe a masallacin Umar Bin Khaɗɗab da ke shatale-talen Dangi kusa da Zoo Road, a Kano.
 
Allah ya kai mu kuma ya bada zaman lafiya da zuriya ɗayyiba.

Loading

Previous Post

Mawallafin jaridun Leadership da A Yau, Sam Ndah-Isaiah, ya rasu

Next Post

Jarumin Kannywood Kabiru Adebo ya yi wa ‘yar sa auren zumunci

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Daga hagu Mahaifin amarya, Kabiru Adebo, Ali Nuhu da Usman Mu'azu a wurin ɗaurin auren

Jarumin Kannywood Kabiru Adebo ya yi wa 'yar sa auren zumunci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!