• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An ba Umar Gombe ragamar shugabancin ‘yan fim na Kano

by DAGA ALI KANO
December 10, 2021
in Labarai
3
Umar Mohammed Gombe, Shugaban riƙon MOPPAN na Kano

Umar Mohammed Gombe, Shugaban riƙon MOPPAN na Kano

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HAƊAƊƊIYAR ƙungiyar masu shirya finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) ta naɗa fitaccen jarumi Umar Mohammed Gombe matsayin shugaban riƙo na reshen ta na Jihar Kano.

Naɗin nasa ya biyo bayan kafa kwamitin shugabanni na wucin gadi na jihar da ƙungiyar ta yi bayan aje aiki da tsohon shugaban ya yi kwanan baya.

A cikin sanarwar da shugaban Hukumar Amintattu (BoT) na MOPPAN, Alhaji Sani Mu’azu, ya bayar a daren yau, ƙungiyar ta bayyana cewa ta yi haka ne domin ta cike gurbin da rashin kwamitin gudanarwa na ƙasa na ƙungiyar ya haifar “a daidai wannan lokaci mai muhimmanci.”

Hukumar Amintattun ta kuma naɗa Hajiya Asma’u Sani a matsayin ɗaya daga cikin shugabannin riƙon “da nufin a ƙara wa kwamitin wakilcin mata”.

Sauran ‘yan kwamitin su ne: Yaseen Auwal, Saima Mohammed, Kamal S. Alƙali da Sulaiman Edita.

Hajiya Asma’u Sani, Memba a kwamitin riƙon shugabancin MOPPAN na Kano

Hukumar Amintattun ta ba ‘yan kwamitin shawarar cewa, “Idan har akwai wani daga cikin su da ya ke da burin tsayawa takarar wani muƙami a zaɓen da za a yi, to ya gaggauta aje aiki tun kafin ya bayyana burin sa.”

Ta ƙara da cewa, “BoT ta ɗauki reshen Jihar Kano da muhimmanci kamar dai yadda ta ɗauki sauran rassan MOPPAN na jihohi, wanda bai kamata a bar shi a baya ba saboda duk wani abu da wani reshe ya aikata, to zai shafi sauran.

“BoT ta yi amanna da cewa kwamitin riƙon zai iya gudanar da zaɓuɓɓuka a jihar, domin ya na da ƙwarewa.

“Babban aikin da aka ba kwamitin riƙon na Umar Gombe dai shi ne ya shirya zaɓen shugabanni na jihar ba tare da wani jan lokaci ba.”

A ƙarshe, BoT ta yi kira ga dukkan membobin ƙungiyar da ma dukkan masu ruwa da tsaki a Jihar Kano da su ba sabon kwamitin riƙon ƙwaryar dukkan goyon baya da haɗin kai da ya ke buƙata domin ya sauke nauyin da aka ɗora masa.

Loading

Tags: hausa filmsMOPPANMotion Picture Practitioners Association of NigeriaUmar Gombezabe
Previous Post

Ibtila’i a Arewa: Mansurah Isah ta kira gangamin karanta Alƙunut

Next Post

INEC ta aika wa Buhari wasiƙar amincewa da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Shugaban Ƙasa Buhari da Shugaban INEC Mahmood Yakubu

INEC ta aika wa Buhari wasiƙar amincewa da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe

Comments 3

  1. ahmedmhussaini2@gmail.com says:
    3 years ago

    Allah Taya Shi Riko

  2. Rufai Yusuf says:
    3 years ago

    Allah ya taimaka

  3. hamma adama says:
    3 years ago

    Allah taimaka yabada ikon yin adalci ameen

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!