• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An yi tir da masu cewa shugaban INEC ya fito takarar shugaban ƙasa

by DAGA ALI KANO
May 9, 2022
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

BABBAN Sakataren Yaɗa Labarai na Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Mista Rotimi Lawrence Oyekanmi, ya bayyana cewa kiran da wasu ke yi wa ogan nasa, Farfesa Mahmood Yakubu, na ya fito ya shiga takarar shugaban ƙasa duk shirme ne.

A cikin ‘yan kwanakin nan akwai masu faɗin cewa wai kada ‘yan Nijeriya su yi mamaki idan su ka ji shi ma Farfesa Yakubu ya shiga da’irar masu neman zama shugaban ƙasar nan a manyan zaɓuɓɓukan da za a yi a 2023.
 A lokacin da ya ke martani kan wannan maganar, Oyekanmi ya ce, “Ba za ta taɓa saɓuwa ba – wai bindiga a ruwa.” 

Ya nanata cewa ogan sa zai ci gaba da kasancewa “alƙalin da ya maida hankalin sa kacokam ga tabbatar da an yi zaɓe fisabilillahi kuma mai nagarta.”

A takardar sanarwar da ya rubuta, sakataren yaɗa labaran ya ce: “An ja hankalin mu ga shaguɓen da wasu ke yi cewa wai kada ‘yan Nijeriya su yi mamaki idan sun ji shugaban INEC ya shiga takarar shugaban ƙasa ko su na kiran sa da ya shiga ɗin. Wannan gurguwar shawara ce. Ba za ta taɓa saɓuwa ba.

“Shugaban zai ci gaba da kasancewa alƙalin da ya maida hankalin sa kacokam ga tabbatar da an yi zaɓe fisabilillahi kuma mai nagarta.  

“Haƙƙin da tsarin mulki ya ɗora masa a matsayin Babban Kwamishinan Zaɓe na Tarayya kuma Malamin Zaɓe a zaɓen shugaban ƙasa muƙamai ne masu daraja da su ka ishe shi da har za a ce ya yi tunanin kaucewa zuwa wani al’amari da ya saɓa wa doka, sanin ya-kamata da kuma aƙidun karan kan sa.

“Shugaban zai ci gaba da sauke nauyin da ke kan shi ba tare da nuna so ko ƙi ga wata jam’iyyar siyasa ko ɗan takara ba.”

Loading

Tags: Dokar ZaɓeFarfesa Mahmood YakubuHukumar Zaɓe ta ƘasaINECRotimi Lawrence Oyekanmishugaban ƙasatakaraTsarin MulkiZaɓen 2023
Previous Post

2023: INEC ta ƙayyade wa jam’iyyu wa’adin kammala zaɓuɓɓukan fidda gwani

Next Post

INEC ba za ta ƙara wa jam’iyyu wa’adin zaɓen fidda gwanaye ba, cewar Yakubu

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Shugaban Hukumar Zaɓe, Farfesa Mahmood Yakubu (a tsakiya), ya na gabatar da jawabin sa a taron (Hoto daga: INEC)

INEC ba za ta ƙara wa jam'iyyu wa'adin zaɓen fidda gwanaye ba, cewar Yakubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!