• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Arewa Jamhuriya Kawai

by DAGA ALHAJI MUDI SIPIKIN
January 18, 2022
in Marubuta
0
Marigayi Alhaji Mudi Sipikin

Marigayi Alhaji Mudi Sipikin

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

1. ‘Yan’uwa na zo in faɗa muku,
Ra’ayi na don ku ji gaskiya.
Bisa waƙar Zungur da yai,
Da ya tsara batun jamhuriya.

2. Wato ta Arewa batun da yai,
Jamhuriya da mulukiya.
Har ma a cikin waƙar ya ce,
Babu damar rushe mulukiya.

3. Ya wo dai zance mai yawa,
Mai daɗi ga kuma gaskiya.
Ya dai dage ya ƙarfafa,
Bisa kan mulki na mulukiya. 

4. Bisa kan hanyar da ya dogara,
Tutocin Shehu abin biya.
Ko ni ma dai na gaskata,
Bisa kan mulki na mulukiyya.

5. Ɗanfodiyo ya ba malamai,
Tutar sa fa don su bi gaskiya.
Su ka ko zauna bisa kan haka,
Bisa kan mulki na mulukiya.

6. ‘Yan baya fa sai su ka shantake,
Su ka sau hanya mai gaskiya.
Su ka dinga biyar son zuciya,
Su ka sa wa kan su rububiya.

7. Sai Gwamna ya zo daga Ingila,
Wani mai gashin bakin tsiya.
Sunan sa fa Lugga ake kira,
Sai ya karɓe tutar gaskiya.

8. Yanzu ma a Kaduna akwai su duk,
A cikin wani ɗaki gu ɗaya.
Sai Gwamna ya ba su fa daftari,
Su ka zama shaiɗanun duniya.

9. In sun hau har da bajujala,
Da su begila duk baki ɗaya.
Ingilish sun ka ɓatar da su,
Su ka bar hanyar mai gaskiya.

10. In ma kai niyyar gaida su,
Sai kai sujjada baki ɗaya.
Haka ma shari’ar su idan ka je,
Sai sun so za su bi gaskiya.

11. Cutar talakawa ta yi yawa,
Wasu ma da yawa sai shan giya.
To don haka ne ban yarda ba,
Bisa waƙar nan ta Sa’adiya.

12. Amma a wajen da ya ce kurum,
Babu damar rushe mulukiya.
Shi ne na taho zan bayyana,
Jama’a ku taho ku ji gaskiya.

13. Asalin Sarki ba gardama,
A cikin Daura ne ka jiya.
Da maciji  ne wani mai faɗa,
Ya fito a cikin wata rijiya.

14. Shi ne asalin kalmar ku san,
Don ku gane zancen gaskiya.
Daga baya ga halin zamani,
Su ka ƙara har da Sarauniya.

15. Kuma rushe gini na mulukiya,
Ya taho mana ba wata kariya.
Ba daɗewa kan ‘yan shekaru,
Za mu tsunduma kan jamhuriya.

16. Ingilishi nan na ƙasar mu duk,
Za su bar mana nan Najeriya.
Wato mulkin kai zai iso, 
Mu fice daga mulkin danniya.

17. Na faɗa na ƙara faɗa muku,
Za mu san mulkin Najeriya.
Ku tuno zancen kuma Ja’afaru,
Sarkin Zazzau mai gaskiya.

18. Ya sa jama’a kishin ƙasa,
Ya nuna nufin Najeriya.
Ga Tafawa-Ɓalewa da yai batu,
Turawa nai mana danniya.

19. Har Aminu na Bauci da yai batu,
Mun sami jawabin gaskiya.
Mun ƙaru da haske mai yawa,
Mun lura da halin duniya.

20. Ingilishi na cutar mu yau,
Mun zamo bayin su a duniya.
Tan gyaɗa wai yau fam sha shida,
Babu imani daga zuciya.

21. Auduga kuwa sai ɗiba su ke,
Ba a zance wannan ko ɗaya.
Haka nan kuza can Jos in ka je,
Ta’ajibi zai cika zuciya.

22. Sun ɗiba sun je sun sayar,
Ramukan sun bar su waje ɗaya.
Ko rufewa ma ba sa kula,
Sun ɓata ƙasar baki ɗaya.

23. Ko’ina sun samu sarakuna,
Sun haɗe kai duk baki ɗaya.
Ba mai magana ko ƙanƙani,
Wa zai magana ai tankiya?

24. Ga mutanen ƙauye sai gwadduna,
Ba abinci bare gun kwanciya.
Abin ajabi ko tausayi,
Sai ka zaga Najeriya.

25. Ko’ina ba kwalta ko kaɗan,
Babu hanya mai kyau ko ɗaya.
Duk Arewa fa sai kwaleji guda,
To bare yunibastin duniya.

26. Ga ta nan wa zai ba mu shi,
Ingilishi na nan Najeriya?
Da dai mulkin en’e duka,
Mai kyau ne ba wata danniya.

27. To me zai sa haka nan da nan,
Har a rushe Sarakin Indiya?
Mulkin su ya zam ya faɗi duk,
Har ƙasar ta zamo jamhuriya.

28. Haka ma a ƙasar nan za a yi,
Hanya kusa ba wata tankiya.
Ni a zato na ma jibi ne,
Ko ko ma gobe da safiya.

29. Shugaba na nan ne zan tsaya,
Ni ne yaron ka na gaskiya,
Ilimin ka ƙwarai da ka bayyana,
Shi ne tsarin Najeriya.

30. Waƙar nan taka haƙiƙatan,
Na yabe ta ƙwarai baki ɗaya.
Kuma ba ni da suka ko kaɗan,
Jumlatan sai baitin nan ɗaya.

31. Ka san ra’ayi ba ya ɓata,
Dole ne in faɗe shi a gaskiya.
Kuma Allah shi ne Shahidi,
Ƙaunar ka na ke duk safiya.

32. Ni ne Mudi daga can Kano,
Unguwar Darma ka ji gaskiya.

Loading

Tags: Aminu KanoArewaDauraGwamna LuggajamhuriyaMudi SipikinSa'adu ZungursarakunaSarkin Zazzau Ja'afaruShehu ƊanfodiyoTafawa-ƁalewaTurawa
Previous Post

Hotuna: MOPPAN reshen Bauchi ta karrama Jamila Nagudu, Bosho da sauran gwarzayen jama’a

Next Post

Zargin satar kuɗin tallafi: Gwamnan Bauchi ya shirga ƙarya, inji Ma’aikata

Related Posts

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 
Marubuta

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 

January 1, 2025
Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 31, 2024
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 20, 2024
Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai

November 30, 2024
Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau
Marubuta

Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau

November 27, 2024
Ƙungiyar matasa da mata za ta naɗa Ado Gidan Dabino Sarkin Mawallafan Arewa
Marubuta

Gasar rubutu: Hukumar Tace Finafinai ta bayyana gwaraza 50 na zagayen farko

November 24, 2024
Next Post
Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq (a hagu), tare da jagorar shirye-shiryen tallafi na ma'aikatar mai kula da Jihar Bauchi, Hajiya Amina Katagum, a lokacin bikin raba takardun kama aiki da kayan aiki ga mutum 300 waɗanda aka horas domin sa ido kan ayyukan tallafi, wanda aka yi a Bauchi a ranar 14 ga Yuni, 2021. (Hoto daga: Ma'aikatar Yaɗa Labarai da Al'adu ta Tarayya)

Zargin satar kuɗin tallafi: Gwamnan Bauchi ya shirga ƙarya, inji Ma'aikata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!