• INEC ta shirya wa zaɓen – Farfesa Yakubu
Oba na Masarautar Benin, Ewuare II, ya bayyana tabbacin cewa ba za a yi wani bala’i a zaɓen gwamna da za a yi a Jihar Edo a ranar 19 ga Satumba ba, akasin yadda wasu ke hangowa.
Shi Oban, wanda shi ne sarkin masarautar, ya yi wannan bayani ne a lokacin da shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya kai masa ziyara a fadar sa tare da wasu kwamishinoni na ƙasa na hukumar a jiya Alhamis.
A cewar Oba na Benin, kada mutane su ji fargabar komai, domin ana ta addu’a da azumi a kan zaɓen.
Haka kuma ya ce kafin ranar zaɓen zai gayyaci ‘yan takarar gwamnan zuwa fadar sa don ƙara nanata yarjejeniyar zaman lafiya da Kwamitin Wanzar da Lumana na Ƙasa, wato ‘National Peace Committee’, zai yi da su kwanan nan a Birnin Benin.
Ya ce: “Mu na kula da duk yadda lamarin ke gudana. Akwai damuwa matuƙa, amma a ƙarshe dai za mu ga haske.
“Mu ci gaba da yin addu’a, domin ta fi bakin bindiga ƙarfi saboda babu matsalar da addu’a ba ta iya warwarewa.
“Kowa na ta yin kiraye-kiraye ga sojojin ruwa da ‘yansanda da sojojin sama sai ka ce wani yaƙi za a yi. Edo ba filin daga ba ce.
“Duk wanda ke so ya jawo rikici ko zubar da jini, to a kan sa abin zai ƙare. Alhaki na nan fa. Na damu da yadda ake ta gudanar da al’amarin.
“Ina kira ga mutanen mu da kada su salwantar da ran su saboda wani mutum. Su waɗanda ke amfani da ‘ya’yan wasu wajen rikici ai ba su barin nasu ‘ya’yan su fito. Idan an kashe ko an raunata waɗanda su ka shiga rikici, su kuwa sai su ci gaba da wawurar kuɗaɗen jama’a.”
Oba na Masarautar Benin ɗin, wanda ya tabbatar da cewar fadar sa ba ta da wani ɗan lele a cikin ‘yan takara a zaɓen, ya shawarci masu zaɓe da su tsaya da kyau su duba ɗan takara kafin su zaɓe shi. Ya ce kada a zaɓi duk wani wanda halayyar sa ba ta da kyau a matsayin wanda zai ɗare kujerar nan mai daraja ta gwamna.
A wani labarin mai kama da wannan, shugaban Hukumar Zabe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa hukumar sa ta shirya tsaf domin gudanar da zaɓen na gwamnan Jihar Edo.
Ya yi wannan bayani mai ƙarfafa gwiwa ne a jiya Alhamis, lokacin da ya ke ganawa da Kwamitin Tuntuɓar Harkokin Tsaron Gudanar da Zaɓe a Benin, babban birnin jihar.
A cewar sa, ya zuwa yanzu INEC ta samu nasarar aiwatar da tsare-tsare har guda 10 daga cikin 14 da ta ƙudiri aniyar aiwatarwa dangane da zaɓen.
Ya ƙara da cewa, “Dalilin wannan ziyara shi ne domin mu ga irin shirye-shiryen da aka fara tun yanzu kafin gabatowar ranar zaɓe. Tabbas, mu na samun dukkan rahotannin shirye-shiryen da ke gudana. Amma duk da haka mu ka ga ya dace mu zo da kan mu, domin gani da idon mu ƙarara.

“Wannan hukuma ta fitar da jadawalin tsare-tsaren yadda matakan zaɓukan Edo da Ondo za su gudana, tun a ranar 6 ga Fabrairu, 2020. Wato kenan mun bayar da sararin watanni kusan bakwai zuwa takwas domin a shirya wa zaɓuɓɓukan biyu sosai.
“To a yau ina farin cikin cewa mun aiwatar da tsare-tsare 10 daga cikin 14 da INEC ta shirya aiwatarwa. Kuma babu wanda aka samu wani tsaikon da har sai da ta kai an sake ɗage ranar da za a aiwatar da shi.
“Abu na ƙarshe shi ne damƙa rajistar gaba ɗayan masu jefa ƙuri’a adadin su baki ɗaya ga jam’iyyu 14 da za su fafata takara.”
Farfesa Mahmood Yakubu ya ce ayyuka huɗu da su ka rage wa INEC sun haɗa buga sanarwar zaɓe da za a yi ranar Talata mai zuwa, gabatar da sunayen ejan-ejan na kowace jam’iyyar da ta shiga takara, duk a rana ɗaya.
“Sai kuma dakatar da kamfen sa’o’i 24 kafin zaɓe. Wato kenan za a dakatar da kamfen da ƙare 12 na daren Alhamis, kafin Asabar ɗin da za a yi zaɓe.
“Saboda haka mu dai sai mu ce mun ma rigaya mun kimtsa, sai jiran zuwan ranar zaɓe kawai.”
Shugaban ya yi tsinkayen cewa zaɓen gwamnan Jihar Edo ne zaɓen farko da INEC za ta fara gudanarwa a lokacin annobar korona.
A kan haka ya ce hukumar zaɓen ta fito da ƙa’idojin yadda za a gudanar da zaɓen a wannan yanayi da ake ciki.

Ya ce, “Mun jaraba tsarin da ƙa’idojin a wani ƙaramin zaɓen cike-gurbi a Jihar Nasarawa. Kuma mun shirya maimaita tsarin a wannan babban zaɓe na Edo.”
Tun da farko, sai da Kwamishinan Zaɓe na Jihar Edo, Mista Johnson Alalibo, ya yi bayanin cewa akwai masu rajista mutum 2,210,534 a Jihar Edo, waɗanda a cikin su 1,159,325 maza ne, mata kuma 1,051,209.
![]()






