A RANAR Asabar, 9 ga Disamba, 2023 aka yi bikin karramawa na ‘Zuma Film Festival’ wanda Hukumar Shirya Finafinai ta Nijeriya (Nigerian Film Corporation) ta saba yi a duk shekara a Abuja. A bikin, wanda ake yi shekara-shekara, wannan hukumar ta Gwamnatin Tarayya ta kan karrama jarumai da kuma fitattun ‘yan Nijeriya da su ka bayar da gudunmawa ga cigaban ƙasa a wani fannin fasahar fim.
A bikin na bana, fitacciyar jarumar Kannywood, Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) ta na ɗaya daga cikin waɗanda aka karrama, ko inda aka ba ta Kyautar Gwarzantaka a Tsawon Rayuwa, wato ‘Lifetime Achievement Award’.
Mujallar Fim ta tattauna da jarumar barkwancin a game da wannan abin farin ciki da ya same ta, kamar haka:
FIM: Kin samu babban kambu na karramawa daga Hukumar Shirya Finafinai ta Nijeriya a taron da ta gudanar. Ki yi wa masu karatun mu ƙarin bayani.
SARATU GIƊAƊO: Wato Allah mai iko kamar yadda ka ce an karrama ni a zaɓen gwaraza da zan kira shi na duniya, don har da ma mutanen Ingila a ciki na gani; sun zo daga Faransa da sauran ƙasashe, duk sun zo, mun yi hotuna ma da su. Kuma ni a Arewa ni kaɗai ce aka zaɓa saboda sun ga cancanta ta a kan irin aiki na na sana’a ta ta fim su ka gayyace ni kamar yadda saƙon ya zo mani ta soshiyal midiya saboda duk yanzu na fi mayar da ayyuka na a kan soshiyal midiya. Don haka duk wanda ya ke so ya yi magana da ni ta soshiyal midiya ake samu na, ba sai an tambayi wani lamba ta ba.

To, don haka wannan gayyatar ma ta Instagram su ka yi mani magana, don haka sai na ji daɗin karramawar saboda ban san su ba, kuma ban taɓa ganin su ido da ido ba; kawai a fim su ka gan ni su ka ga cancanta ta ba tare da sun bi ta hannun kowa ba, su ka bi ta shafi na na Instagram mu ka yi magana har su ka turo mani kuɗin jirgi su ka samar mani da masauki. Kuma kafin wannan sun turo mani da katin gayyata na ranar da za a yi, kafin wata guda a yi taron, amma ban sanar ba saboda halin rayuwa, sai ranar da za a yi na sanar.
Kuma a yanzu Allah ya sa mun je an yi taro an tashi lafiya na dawo gida na tare da kambun karramawa da aka ba ni.
FIM: Da yake jama’a ne masu yawa aka karrama, ko yaya ki ka samu kan ki a cikin wannan taron?
SARATU: To, gaskiya kamar yadda na faɗa maka ni kaɗai ce daga Arewa a fannin sana’ar mu, haka ma mutum ɗaya ne daga Kudu wanda shi bai samu zuwa ba, kuma duk wasu harkokin rayuwa daga Arewa ma ni kaɗai ce na je wanda aka karrama, sai dai waɗanda aka gayyata. Don haka na ji daɗin wannan karramawar sosai, saboda na wakilci Arewa kuma na wakilci Kannywood. Don haka wannan abin alfahari ne a gare ni.

FIM: Ba a wannan ba ne ki ka fara samun kambu na karramawa. Me ya bambanta wannan da waɗanda ki ka samu a baya?
SARATU: E haka ne, na sha samun karramawa, ina ganin tun da na shiga harkar fim ma na ke samun hakan. Yau shekara 23 kenan ina samun kyaututtukan karramawa daga ɓangarori na jama’a da dama. Amma dai wannan shi ne mafi girma da na samu, saboda shi ne aka kira ni har zuwa Abuja don a karrama ni kuma aka haɗa mu da manyan mutane na duniya aka aka karrama mu. Kuma shi ma kambun karramawar na musamman ne, don haka zan iya cewa wannan shi ne mafi girman karramawa da na samu a yanzu; ban san nan gaba ba ko za a kira ni zuwa Ingila da Amurka don a karrama ni.
Kuma alhamdu lillahi wannan ya ƙara mani ƙarfin gwiwar da na samu da zan ci gaba da harkar fim da aka san ni da ita, domin irin wannan shi ne ya ke ƙara wa irin mu ƙarfin gwiwa saboda ba don mun san wani ko wata hanya ba, kawai Allah ne ya sa aka ga mun cancanta aka ba mu, saboda an ga yadda na ke a cikin harkar fim, na mayar da abin sana’a ba wai na ɗauki abin da wasa ko wata kwalliya ba, kawai ina sana’a ne don na samu kuɗi na gudanar da rayuwa ta cikin mutunci.

Don haka ina kira ga abokan sana’a ta ‘yan fim, su daure su ci gaba da ƙwazo kamar yadda mu ke yi, don su ma wata rana za a kira su a ba su wannan karramawar, domin kafin a ba ni na san an bai wa waɗansu. Amma a wannan shekara ta 2023 Saratu Giɗaɗo (Daso) aka bai wa wannan babbar karramawa. Don haka su ci gaba da bada ƙwazo su ɗauki wannan sana’ar a matsayin sana’ar su, kada a ɗauke ta don neman suna, don ba a yin suna sai an zama gwarzo.
Sannan ina kira ga mutanen waje da su ke kallon mu duk waɗanda su ke zagin mu sudaina. Idan ka na kallon sana’ar mu a matsayin marar kyau, to kai ma a wajen wani taka sana’ar ba mai kyau ba ce, don haka mu rinƙa yi wa junan mu adalci mu na fatan Allah ya yi mana jagora.
FIM: To, madalla mun gode.
SARATU: Ni ma na gode.
