FITACCEN jarumin Kannywood, Malam Umar Sani Jigirya, ya bayyana cewa ya ci gaba da harkokin sa a ɓangaren aikin rediyo bayan an cire shi daga diramar ‘Daɗin Kowa’ ta gidan talbijin na Arewa 24, inda ya riƙa fitowa da sunan Sallau.
Tun bayan da aka daina ganin sa a shirin, mutane dama sun yi ta tambayar ko ina ya shiga?
A tattaunawar da ya yi da mujallar Fim kan halin da ya ke ciki a yanzu, Jigirya ya nuna cewa ko kaɗan bai tagayyara ba bayan ya bar shirin.
Ya ce, “To shi da man shirin ‘Daɗin Kowa’ ba ni na samar da shi ba, na wasu ne da su ka samar da masu rubutun labari su ka rubuta masu, su ke ɗaukar ma’aikata kuma ni ma sai ya zama ina cikin wanda labarin ya kira ni, su ka ga na dace da shi su ka ɗauke ni a daidai lokacin da labarin ya kira ni.
“Domin ai ka ga a farkon shirin ‘Daɗin Kowa’ babu Sallau, sai daga baya Sallau ya shigo, kuma ana tafiya Sallau ya je gaɓar da babu shi. Kusan sau biyu ko uku Sallau ya na tafiya ya na dawowa.

“To, wannan yanayi ne na labarin da su masu rubutun za su duba su ga a ina mutum ya dace ya fito, a ina ya dace a ajiye shi. Wani ma za ka ga kashe shi ake yi a labarin. To, duk yanayi ne ya ke zuwa da haka, don haka ko da an ga a yanzu babu Sallau a cikin shirin ‘Daɗin Kowa’, to labarin ne ya zo da haka.
“Ta yiwu kuma nan gaba labarin ya dawo da Sallau ko kuma ya tafi kenan.”
Dangane da ko a ina ya sa gaba a yanzu kuwa, sai jarumin ya ce, “To da man ni ina aikin jarida, don na yi aiki a gidan Rediyon Rahama, sannan na yi aiki a gidan Rediyon Arewa, sannan kuma kusan shekara talatin ni ɗan fim ne da na fara tun ana wasan daɓe.
“Don haka a yanzu ina yin harkokin da su ka shafi rediyo da fim da tallace-tallace. Kai, har ma siyasa ina yi tun a lokacin baya! Don haka ba na tsaya ba ne ina yawon maula.
“Sannan akwai tashar TV ta YouTube da na buɗe, Jagora TV, da na ke saka finafinan da na yi. Kuma ana gayyata ta zuwa wasu finafinan.
“To ka ga ba za a ce an rasa inda aka dosa ba. Da man dai a rayuwa bai kamata a ce mutum ya tsaya ya na kallo da ido ɗaya ba, kamata ya yi mutum ya kalli ko’ina don ya gano idan babu wannan waje ina kuma zan yi amfani da damar da na samu.
“Domin idan mutum ya yi amfani da damar da ya samu, to abin da zai samu a gaba ya fi kuɗin da za a biya shi idan ya yi aiki.
“Don haka ni ina ganin wasu ne su ke wasa da damar su idan su ka samu, kuma idan ta tafi sai su rasa abin da ya kamata su yi.”
Jigirya ya yi kira ga ‘yan fim da su riƙa amfani da damar da ta zo masu, domin babu wani abu da ya ke ɗorewa.