• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Batun zanga-zanga: Minista na so jama’a su ƙara haƙuri domin Tinubu yana ƙoƙarin rage matsi 

by WAKILIN MU
July 22, 2024
in Nijeriya
0
Jaridar Daily Trust ta saba buga ‘rahotannin ƙarya’, inji Gwamnatin Tarayya

Alhaji Mohammed Idris

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya, musamman matasa masu shirin zanga-zanga, da su yi haƙuri.

A halin yanzu wasu ‘yan Nijeriya na ta yin shelar cewa za su yi zanga-zangar lumana a ƙarshen wannan watan domin bayyana ɓacin ran su kan matsin tattalin arziki da ake fuskanta a yau.

A wata hira da ya yi da BBC Hausa a ranar Asabar, ministan ya ce Gwamnatin Tarayya ta ɗauki wasu muhimman matakai domin magance matsalolin da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

Ya ce: “Akwai mataki na farko da gwamnati ta ɗauka na a samu a raba kayan abinci ga al’ummar Nijeriya. An kai shinkafa jihohi duka ga baki ɗaya talatin da shida da kuma yankin Abuja.”

Ya ƙara da cewa, “Akwai wani shiri da ake yi na CNG, ma’ana wannan harka na iskar gas wanda duk motocin da za su yi aiki za su yi aiki da wannan na’ura, wato na iskar gas, ma’ana misali idan kana kashe naira goma wajen sufuri yanzu kuɗin ka zai dawo ƙasa ma da naira huɗu. Ka ga an sake samun cigaba.

“In ka lura da abin da ake yi kamar na bututun gas na AKK wanda kwanakin baya an je Kaduna an sake duba shi, ya kai kusan wato kashi casa’in da biyar da gamawa. Abu ne da aka fara tun waccan gwamnatin da ta shuɗe.

“Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da kuma ya tsaya tsayin daka lallai a samu a gama wannan shiri saboda idan aka yi shi za a samu sauƙi sosai.

“Duk kamfanonin da aka rurrufe saboda matsalar wutar lantarki da ɗimbin al’umma da suka rasa ayyukan su saboda rufe kamfanunnuka idan Allah ya yarda za su dawo.”

Ministan ya yi nuni da cewa Shugaban Ƙasa ya ƙaddamar da Shirin Lamunin Ɗalibai don ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi su samu damar zuwa makaranta.

Ya ce: “Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya kuma ƙaddamar da harkar wato abin da ake ce ma Student Loan, wato bashi saboda a yi makaranta. Yana takaicin cewa bai kamata a ce wani yaro bai iya zuwa makaranta ba saboda iyayen sa ba su da kuɗin biya masa makaranta.

“Yanzu duk wani wanda ya iya cin jarabawa, duk wani yaro ɗan Nijeriya, cikakken ɗan Nijeriya da ya iya cin jarabawa, zai iya zuwa ya amfana a biya masa bashi mai sauƙi cikin rahusa ya biya kuɗin makaranta, ba ma kawai a biya kuɗin makaranta ba, ya samu kuɗin da kuma zai iya ɓatarwa har ya gama karatun sa.”

Dangane da wahalhalun da ‘yan Nijeriya ke fuskanta duk da alƙawurran da Shugaba Tinubu ya yi na kawo sauƙin rayuwa, Idris ya ce: “Lallai gwamnati ta yarda cewa akwai wannan matsatsi. Abin da ya bambanta gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatoci da yawa shi ne idan akwai matsala akan amsa a ce lallai akwai matsala a wuri kaza amma kuma ga abin da mu ke yi na a samo maslaha.

“A yanzu maganar da ake yi a harkar tsaro abin da muke ciki misali shekara ɗaya baya, ko shekara biyu baya, ai ka ga abin ba haka ba ne.

“Mu na fata a haɗa ƙarfi da ƙarfe, su mutanen ƙasa su ba gwamnati goyon baya domin a kawo ƙarshen wannan al’amari.

“Saboda haka a ƙara yin haƙuri, kiran da gwamnati ke yi kenan. A ƙara yi wa gwamnati haƙuri, idan Allah ya yarda a hankali a hankali za a kawo ƙarshen wannan al’amari.”

Ministan ya ce akwai tanadi da gwamnati ta yi wa manoma inda Babban Bankin Nijeriya (CBN), ta hanyar Ma’aikatar Aikin Gona, ya raba taki buhu miliyan dubu ɗari ɗaya da hamsin ga manoma.

Loading

Tags: Bola Ahmed TinubuMohammed Idristattalin arzikizanga-zanga
Previous Post

Jarumin Kannywood, Sulaiman Alaƙa ya kwanta dama

Next Post

Batun zanga-zanga: Wasu ɓata-gari na iya amfani da damar su tada tarzoma – Idris 

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Batun zanga-zanga: Wasu ɓata-gari na iya amfani da damar su tada tarzoma – Idris 

Batun zanga-zanga: Wasu ɓata-gari na iya amfani da damar su tada tarzoma - Idris 

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!