FITACCEN mawaƙi Ado Isah Gwanja, wanda ake yi wa laƙabi da Limamin Mata, ya sake bugo wata sabuwar waƙa bayan waƙar sa ta ‘Warr’.
Alamu na nuna cewa Gwanja na neman zama sarki a wannan shekarar, domin kuwa ‘Warr’ ita ce waƙar da babu kamar ta wajen fice a bana a arewacin Nijeriya.
Waƙar ‘Warr’ ta bazu kamar wutar bazara, kowane lungu da saƙo ka shiga za ka ji ta ta na tashi a wurin manya da yara.
Haka in ka shiga kafafen sada zumunta da kuma wuraren da ake biki.

A cikin waƙar babu inda ya fi ɗaukar hankalin mutane kamar baitin, “Za ki zo ne ko ko ba za ki zo ba? Za ni zo, bari in shafa hoda. Ko kin zo da ke da hodar uban ku zan ci.” Mujallar Fim ta gano cewa ya ɗauko wannan baitin ne daga tsohuwar waƙar ‘Asauwara’ ta Mamman Shata.
A cikin kwanakin nan kuma sai ga mawaƙin ya sake zuwa da wata waƙar kuma mai taken ‘Cass’, ga shi kuma shauƙin ‘Warr’ bai gama fita daga jikin masoyan sa ba, sai sabuwa ta kunno kai da ƙarfin ta.
Yau kwanaki uku zuwa huɗi kenan, duk inda ka leƙa musamman TikTok, Status na WhatsApp da kuma Instagram na mata waƙar ake yayi, tun bayan sakin gajeren bidiyo da Gwanja ya yi ya na mamin ɗin waƙar a situdiyo.
Ganin yadda waƙar ta karɓu nan da nan, wasu ke ganin cewa sabuwar waƙar za ta fi ‘Warr’ karɓuwa, saboda ta zo da wani salo irin nata. Wasu na ganin cewa ba lallai ba ne ‘Cass’ ta yi karɓuwar da ‘Warr’ ɗin ta yi.
A halin da ake ciki yanzu dai Ado Gwanja ya bar masoyan sa da muhawara kan waƙoƙin biyu. ‘Warr’ ɗin ce ko ‘Cass’?