ALAMU sun nuna cewa mai ɗaukar sauti a Kannywood, Bilal Muhammad Naseer, shi ne wanda zai fara buɗe ƙofar aure a Kannywood a cikin sabuwar shekarar nan.
A ranar Asabar, 7 ga Janairu, 2023 za a ɗaura auren Bilal, wanda wasu ke kira ‘Lion’, da masoyiyar sa Jamila Isah Muhammad.
Za a ɗaura auren da misalin ƙarfe 2:00 na rana a gida mai lamba L.I. 18, Fulani Road, kusa da Ramadan Hospital, unguwar Nassarawa, Kaduna.

Da misalin ƙarfe 8:00 na dare kuma za a gudanar da walima a Marafa Road da ke unguwar Ɗirkaniya, Kaduna.
Kafin ranar ɗaurin auren, a ranar Juma’a za a buga wasan ƙwallon ƙafa a filin wasa na Kadwell da ke Barnawa.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa Bilal shi ne yaron da tsohon mai ɗaukar sauti kuma jarumi a Kannywood, Shamsu Ɗan-Iya ya koya wa aikin ɗaukar sauti.
