SHUGABAN Ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa shugabannin sabuwar Hukumar Kula Da Naƙasassu ta Ƙasa, wato National Commission for Persons with Disabilities, kamar yadda Dokar Hana Wariya Ga Naƙasassu ta 2019 ta tanadar.
Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Mista Femi Adesina, shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya bayar a ranar Litinin.
Hukumar za ta kasance ne a ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Agaji tare da Jinƙai ta Tarayya inda a yanzu Hajiya Sadiya Umar Faroukh ta ke minista.
Dokar dai ta tanadi cewa za a samar da shugaba tare da membobi shida waɗanda dukkan su naƙasassu ne daga sassan ƙasar nan guda shida waɗanda za su jagoranci Majalisar Gudanarwar hukumar na tsawon shekara huɗu, kuma za a iya ƙara masu wa’adin shekara huɗu na ƙarshe, tare da amincewar Majalisar Dattawa.
Haka kuma dokar ta ce za a naɗa Babban Sakatare, wanda ke ƙarƙashin Majalisar Gudarwar, don aiwatar da ayyuka da tsare-tsaren hukumar, wanda kuma shi ma tilas ya kasance naƙasasshe ne, kuma zai yi wa’adin shekara biyar, sannan za a iya daɗa masa wa’adin shekara biyar na ƙarshe.
Sanarwar daga fadar shugaban ƙasa ta bada sunaye da muƙaman waɗanda aka naɗa da kuma yankin da su ka fito, kamar yadda shugaban ƙasan ya amince. Su ne kamar haka:
Hon. Dakta Hussaini Suleiman Kangiwa – Shugaba – daga Arewa-Maso-Yamma
Oparaku Onyejelam Jaja – Memba – Kudu-maso-Gabas
Philomena Isioma Konwea – Memba – Kudu-maso-Kudu
Omopariola Busuyi Oluwasola – Memba – Kudu-maso-Yamma
Amina Rahma Audu – Memba – Arewa-maso-Yamma
Mrs Esther Andrew Awu – Memba – Arewa-ta-Tsakiya
Abba Audu Ibrahim – Memba – Arewa-maso-Gabas
James David Lalu – Babban Sakatare – Arewa-ta-Tsakiya
![]()





