• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cika shekara 22 da rasuwar Mamman Shata

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
June 18, 2021
in Mawaƙa, Nijeriya
0
Cika shekara 22 da rasuwar Mamman Shata
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A YAU, 18 ga Yuni, 2021 Alhaji Dakta Mamman Shata Katsina, MON, ya cika shekaru 22 da komawa ga Mahaliccin sa. A halin da ake ciki yanzu Shata ya zame wa makaɗa da mawaƙan Hausa dutse ba ka ɗaukuwa sai da gammo, mutsu-mutsu gobe jar kasa, ruwan dare mai gama duniya, ya buga da mazajen farko ga shi ya na bugawa da mazajen yanzu. Abin da maroƙan sa ke faɗa kenan idan zai fara waƙar sa ta Bakandamiya.

Babu wata ƙasa a duniya da za ta bugi ƙirji ita kaɗai ta ce ta samu cigaba a rana guda. Su kan su ƙasashen da su ka ci gaba irin su Amurka, Rasha, Chaina, Birtaniya, Japan da Jamus sun yi amfani ne da kyawawan al’adun su wajen gina tushen cigaban da su ka samu.

Mawaƙa da makaɗan waɗannan ƙasashe da su ka ci gaba sun bada gudunmawa mai yawan gaske ta fuskar irin tasu fasahar wajen ciyar da ƙasashen nasu gaba.

Farfesa Ɗandatti Abdulƙadir, kafin ya zama Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero, Kano, ya rubuta kundin digirin sa na uku ne kan rayuwa da waƙoƙin Alhaji Mamman Shata, wanda ya gabatar ga shaihunan malaman Jami’ar Indiana ta ƙasar Amurka. Wannan yunƙuri na Frfesa Ɗandatti ya ƙara tabbatar da cewa shaharar da Shata ya yi, ba a iya Nijeriya kawai ta tsaya ba har ma da waɗansu ƙasashen.

Cikakken sunan Shata shi ne Muhammadu Lawal. Sunan Mamman laƙabi ne irin wanda kakanni kan raɗa wa jikokin su tun su na yara. Ita kuwa kalmar “Shata”, laƙani ne wanda ake kiran sa da shi lokacin da ya ke cinikin goro. Magaji Salamu Musawa, wanda a lokacin kamar uba ne ga Shata, shi ya raɗa masa sunan “Mai Shata”. Manufar sa ita ce mutum wanda in ya samu abu sai ya ɓatar abin sa, ba ya tattali.

Kafin zuwan Turawa ƙasar Hausa, al’ummar Hausawa na da addinin su na Musulunci, akwai kuma kaɗan da ke bin addinin gargajiya da ake kiran su Maguzawa. Ba a san hikimar rubuta sunayen yara da shekarun su a ajiye don tarihi ba kamar yadda yanzu ake yi. Wannan shi ya sa ba a san cikakkiyar shekarar da za a ce an haifi Alhaji Mamman Shata ba. Amma a shekarar da ya kai ziyara gidan rediyon Muryar Amurka (VOA) a cikin 1989, ya ce shekarun sa 65 a lokacin. Manazarcin tarihin rayuwar Shata, Ibrahim Sheme, ya ƙiyasta a cikin littafin ‘Shata Ikon Allah!’ cewar an haife shi ne a wajen 1923.

Kwalin faifan garmaho na waƙoƙin Shata

Shata ya yi waƙoƙi bila adadin waɗanda har zuwa yanzu tarihi bai kai ga gano yawan su ba. Haka waƙoƙin sa da su ka yi shuhura su ma ba su ƙirguwa, amma ga guda 20 waɗanda mujallar Fim ta zaƙulo domin kafa misali, su ne:

1. ‘Na Gode Wa Bashar Ɗan Musa Mamman Mai Mulkin Daurawa’

2. ‘Na Tsaya Ga Annabi Muhammadu’

3. ‘Ƙusoshin Birni Uwawu’

4. ‘Umaru Ɗan Ɗanduna Na Gwandu’

5. ‘Sarkin Bori Sule’

6. ‘Wamban Kano Habu Ɗan Maje’

7. ‘Bawan Allah Mamman Ɗa’

8. ‘Gagarabadan Namiji Tsayayyen Ɗan Kasuwa’

9. ‘Alhaji Garba ‘Yammama’

10. ‘Sardauna Kakan Ka Ɗanfodiyo, Jikan Gidan Bello Ne Ahmadu’

11. Na Gode Wa Hassan Hadi’

12. ‘Jirgin Sama Bawa Tashi Ƙoli Ka Tsere Na Laraba’

13. ‘Yarinya Lami Shagamu’

14. Na Gode Goshi Ta Ɗangude’

15. Bakandamiya

16. ‘Haji Gaban Bichi Ɗan Shehu’

17. ‘Na Gode Wa Amadun Gaya’

19. Waƙar Indon Musawa

20. ‘Ta Kunya Delun Kunya’

To sai dai al’umma da manazarta a manyan jami’oi’n ƙasar nan, musamman ɓangaren nazarin harshen Hausa, na cigaba da nazarce-nazarce bisa irin gudunmawar da Shata ya bai wa harshen Hausa ta hanyar waƙoƙin sa. Da alama ba za a daina yin nazarin waƙoƙin Shata da rayuwar sa ba har ƙasa ta naɗe.

Loading

Tags: Alhaji Mamman ShataHausa musicmawakan hausa
Previous Post

An ɗaura auren jaruma Naja’atu Muhammad da ɗan ƙwallo Abdullahi Shehu

Next Post

Cika shekara 22 da rasuwa: Muhimman bayanai 22 dangane da Shata

Related Posts

Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar
Mawaƙa

Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar

December 11, 2025
Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Next Post
Cika shekara 22 da rasuwa: Muhimman bayanai 22 dangane da Shata

Cika shekara 22 da rasuwa: Muhimman bayanai 22 dangane da Shata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!