DARAKTA kuma jarumi a Kannywood, Ibrahim Usman Muhammad, wanda aka fi sani da Al-Imash, ya ƙara aure.
A ranar Juma’a, 29 ga Disamba, 2023 aka ɗaura auren Al-Imash da masoyiyar sa, Ruƙayya Halliru Goma Ibrahim, a Masallacin Juma’a na Malali, Kaduna, da misalin ƙarfe 1:30 na rana bayan idar da sallar Juma’a, a bisa sadaki N100,000.
An yi walima a ofishin angon wanda ke Amal Complex, Kaduna, wanda uwargidan sa, Hajiya Binta Lugga, ta ɗauki nauyi.

Wasu daga cikin waɗanda su ka halarci ɗaurin auren sun haɗa da Usman Babangandu, Habibu Sanyi-Sanyi, Isma’il FKD, Ɗanladiyo Mai Atamfa, Lawal Mai Atamfa, Isma’il I.Z., Babangida Akto, Hamisu Bawasa, Abba D. Malam, Abdul FKD, Salisu MJB, Abubakar MGB, Ɗayyab Maiɗa’a, Ahmad Rarara, Jibril Ɗanbakano, da Ɗanjummai C.V.
Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.