• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Dattawan Arewa sun ƙalubalanci Gwamnan Binuwai kan kalaman ƙyamar Fulani

by DAGA KAMAL ALIYU SABONGIDA
November 11, 2022
in Nijeriya
0
Gwamna Samuel Ortom

Gwamna Samuel Ortom

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR Dattawan Arewa (Northern Elders Forum, NEF) ta bayyana kalaman da Gwamnan Jihar Binuwai, Mista Samuel Ortom, ya yi a matsayin ‘masu tsauri’, wanda a lokacin da ya ke yin Allah-wadai da kisan mutane 18 da aka yi a yankin karamar hukumar sa a ranar Juma’a da ta gabata ya ce ba zai taba goyon bayan wani Bafulatani ya sake zama shugaban ƙasar Nijeriya ba. 

Ortom ya bayyana haka ne a lokacin da ya ke karbar bakuncin takwarorin sa na jihohin Ribas, Oyo, Abiya da Inugu a wajen wata liyafar cin abinci a Makurdi. 

Ya ce: “Ku na so in zama bawa ga Bafulatani. Gara in mutu. Ana kashe mutane na, ku na so in yi shiru. Ba zan taba goyon bayan Bafulatani ya zama shugaban kasa ba. Idan kuma akwai wani wanda ya ke shirye ya yi aiki tare da ni don tabbatar da tsaron jama’a ta, zan yi aiki da shi.”

Sai dai Ƙungiyar Dattawan Arewa, a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labarai na ƙungiyar, Dakta Hakeem Baba-Ahmed, ta ce kalaman gwamnan kwata-kwata ba su dace da shugaba ba, musamman a daidai lokacin da ake siyasantar da matsalar rashin tsaro a kasar nan.

Ƙungiyar ta ce, “Mu ma, kamar sauran ‘yan Nijeriya, mun kalli bidiyon da Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom, ke magana a cikin yanayi da kuma yare da bai dace da shugaba ba.

“Ƙungiyar Dattawan Arewa ta ci gaba da yin Allah-wadai da yanayin ƙawanya da rashin tsaro da ‘yan Nijeriya su ka yi rayuwa a ƙarƙashin su a cikin ‘yan shekarun nan, musamman a Arewa ‘yan damfara Fulani sun yi fice a matsayin masu kisa da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

“Ya kamata Gwamna Ortom ya cika rantsuwar da ya yi da kuma alƙawarin da ya yi na yin rayuwa a matsayin sa na shugaban al’ummar sa. 

“Ya kamata ya guje wa sha’awar buga wasan kwaikwayo wanda, kamar sauran ‘yan Nijeriya, ke da burin samun sauƙi da kuma kawo karshen kashe-kashen da ke tayar da juna da kuma kai su ga rikice-rikice marasa iyaka.”

Loading

Tags: BinuwaiFulaniHakeem Baba-Ahmedkashe-kasheƘungiyar Dattawan Arewarashin tsaroSamuel OrtomZaɓen 2023
Previous Post

PDP kaɗai ce jam’iyya a Nijeriya, APC na kakarin mutuwa – Atiku

Next Post

Najib Marubuci da Khadija sun angwance

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Ango Najib da amarya Khadija

Najib Marubuci da Khadija sun angwance

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!