• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 11, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Tarayya ta musanta iƙirarin Binance na neman cin hanci

by WAKILIN MU
May 8, 2024
in Nijeriya
0
Gwamnatin Tarayya ta musanta iƙirarin Binance na neman cin hanci

Alhaji Mohammed Idris

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Tarayya ta mayar da martani kan iƙirarin da Shugaban kamfanin Binance, Richard Teng, ya yi na cewa wai wasu jami’an gwamnatin Nijeriya sun buƙaci a ba su cin hanci da kuɗaɗen kirifto don warware binciken laifuffukan da ake yi wa masa.

Teng ya yi wannan iƙirarin ne a wani shafin yanar gizo wanda kafafen watsa labarai na ƙasashen waje suka buga ranar Talata, inda ya ƙara da cewa lauyan Binance ya ƙi amincewa da tayin.

Da yake mayar da martani kan zargin a ranar Laraba, Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Teng ya ƙare da “dabarun karkatar da hankalin jama’a da kuma yunƙurin yin ɓatanci da kamfanin ke yi don kawar da tuhume-tuhume masu tsanani da yake fuskanta a Nijeriya.”

A wata sanarwar da Rabiu Ibrahim, mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai ya sanya wa hannu, ministan ya jaddada cewa wanda ya kafa Binance, Changpeng Zhao, ya aikata irin wannan laifin na halasta kuɗaɗen haram a Amurka, kuma a halin yanzu yana zaman gidan yari, lamarin da ke nuni da cewa ya kamata kamfanin na kirifto ya miƙa kan sa ga hukuma domin bincike.

Ya ce: “Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta na sane da yunƙurin da Binance ke yi na wanke sunan sa a matsayin kamfanin da ba ya bin ƙa’ida da dokokin da ke jagorantar harkokin kasuwanci a ƙasashe masu cin gashin kai.

“A cikin wani saƙon da ya wallafa a shafin yanar gizo wanda yawancin kafafen watsa labarai na ƙasa da ƙasa su ka wallafa a yanzu, Shugaban Binance Richard Teng, ya zargi kan wasu jami’an gwamnatin Nijeriya da ba a san ko su waye ba da cin hanci da rashawa, wanda ya yi iƙirarin cewa sun buƙaci a biya kuɗaɗen kirifto dala miliyan 150 don warware binciken laifuffukan da ake yi wa kamfanin.

“Wannan iƙirarin na Shugaban Binance ba gaskiya ba ne. Ba komai ba ne illa dabarar karkatar da hankalin jama’a da kuma yunƙurin yin ɓatanci da kamfanin ke yi don kawar da tuhume-tuhume masu tsanani da yake fuskanta a Nijeriya.

“Gaskiyar wannan al’amari ita ce ana binciken Binance a Nijeriya ne saboda yadda ya ba da damar yin amfani da dandalin sa wajen halasta kuɗaɗen haram, bayar da tallafi ga ta’addanci, da kuma tafka maguɗin kuɗaɗen ƙasashen waje ta hanyar cinikin haramun.”

Loading

Tags: Binancecrypto currencykiriftoMohammed IdrisRichard Teng
Previous Post

Ni na fara sa Ali Nuhu a fim, amma ana yaɗa ƙarya a tarihin shi – Sani Muhammad Sani

Next Post

Shigar Ali Nuhu harkar fim: Akwai gyara a iƙirarin Sani Muhammad Sani, inji darakta Salisu Mu’azu

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Shigar Ali Nuhu harkar fim: Akwai gyara a iƙirarin Sani Muhammad Sani, inji darakta Salisu Mu’azu

Shigar Ali Nuhu harkar fim: Akwai gyara a iƙirarin Sani Muhammad Sani, inji darakta Salisu Mu'azu

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!