• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gyaran Dokar Zaɓe: Har yanzu Majalisar Tarayya ba ta amince da wasu manyan muradai ba – INEC, Yiaga Africa

by DAGA WAKILIN MU
September 18, 2021
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da ƙungiyar Yiaga Africa sun bayyana cewa har yanzu Majalisar Tarayya ba ta amince da wasu muhimman buƙatu da aka tura mata ba dangane da yi wa Dokar Zaɓe garambawul. 

Sun bayyana haka ne a ranar Juma’a a wajen taron masu ruwa da tsaki kan lamarin gyaran Dokar Zaɓe, wanda Yiaga Africa da haɗin gwiwar Majalisar Tallafa wa Tsarin Dimokiraɗiyya a Nijeriya na Tarayyar Turai, wato ‘European Union Support to Democratic Governance in Nigeria Project’ (EU-SDGN) a Abuja.

Babban Kwamishinan INEC kan Yaɗa Labarai, Mista Festus Okoye, wanda Mataimakin Daraktan Tsara Dokoki na INEC, Mista Oluwatoyin Babalola, ya wakilta, ya ce hukumar ta lura da wasu ‘yan matsaloli a ƙudirin yi wa Dokar Zaɓen garambawul duk da yake abuvuwa ne na cigaba.

Okoye ya ce a bisa hakan, hukumar ta kawo shawarar gyararraki kimanin 98 da za a yi wa Dokar Zaɓen amma ba dukkan su aka amince da su ba, misali batun sakin kuɗi da wuri, shirya jadawaɗin aikin rajistar masu zaɓe da wuri, da sauran su, waɗanda ba a amince da su ba tukuna, duk da yake an ɗan samu cigaba.

Ya ce, “Ƙudirin ya ba mu ikon mu yi amfani da na’urar karanta kati mai ƙwaƙwalwa (smart card readers) da sauran kayan kimiyya da zaɓe ta hanyar intanet and amma kuma ƙudirin daga Majalisar Dattawa bai ba mu ikon mu aike da sakamakon zaɓe ba.

“Duk da waɗannan abubuwan, akwai waɗansu sassa da ba a amince da su ba kuma mun yi amanna da cewa idan aka amince da su, zai taimaka wajen haɓaka ingancin zaɓe.

“A Sashe na 68 na Dokar Zaɓe, hukumar ta buƙaci a karɓi shawarar sake nazarin bayyanawa tare sa dawo da sakamakon zaɓe daga jami’an kawo sakamako (returning officers) wanda aka yi ba bisa ƙa’ida ba, kamar misali bayyana sakamakon da aka yi ta hanyar tilastawa a sake duba shi, amna ba a amince da wannan ba.

“Na biyu, mun buƙaci cewa a sauya mana Sashe na 143 na Dokar Zaɓe wanda ya ba suk wani mai cin moriyar zaɓe da aka soke damar ya ci gaba da riƙe muƙami har zuwa lokacin da aka gama shari’ar ɗaukaka ƙara saboda kada mu dinga bada satifiket ɗin amincewa da wanda aka zaɓa mu na kuma sakewa.

“Haka kuma hukumar ta kalli batun aikawa da sakamako a matsayin babban al’amari, hanyar fasaha na ƙara bunƙasa, idan an aika da sakamakon zaɓe, zai inganta sahihancin zaɓe kuma ya rage yin katsalandan, amma ba a amince da waɗannan ɗon ba.’’

Daraktar Shirye-shirye ta Yiaga Africa, Cynthia Mbamalu, ta yaba wa ƙudirin neman garambawul ɗin saboda wani cigaba da aka samu a wasu sassa kamar misali wajen shigar da kalmar da ta shafi jinsi wato “shi ko ita”, da tura kuɗi da wuri don tabbatar da ingancin gudanarwar INEC, sassauƙan tsarin rajistar masu zaɓe, shigo da naƙasassu, da sauran su.

Saboda haka Mbamalu ta yi kira ga shugabannin Majalisar Tarayya da su gaggauta kafa kwamitocin tuntuɓa da za su zauna su fito da ƙasida ɗaya kan ƙudirin yi wa Dokar Zaɓen garambawul kamar yadda aka riga aka zartar.

Mbamalu ta ce ta hanyar yin hakan, ana ba ‘yan majalisar shawarar su sake duba matsayar su kan wasu daga cikib  shawarwarin da jama’a da masu ruwa da tsaku su ka kawo masu, waɗanda an tsallake wasu, of ki an siyasantar da su  ko sun zama abin muhawara.

Ta ce abu muhimmi shi ne tilas ne kwamitin tattaunawar ya yanke hukunci a bisa muradin jama’ar ƙasa wajen amincewa da gyarw-gyare inda dukkan zaurukan majalisar biyu su ka ɗauki mabambantan ƙudiri don ganin an riƙa yin zaɓuɓɓuka fisabilillahi.

Dakta Ajibola Basiru, shugaban kwamiyin yaɗa labarai na Majalisar Dattawa, ya yaba wa Yiaga Africa saboda tsarin da ta fito da shi, ya ƙara da cewa hanya ɗaya da za a ci gaba da multin dimokiraɗɗa ita ce su tabbatar da cewa akwai nagarta da karɓuwa ga jama’a wajen aikin dimokiraɗiyya wanda shi ne ya kawo mutane zuwa kan dokin shugabanci.

Loading

Tags: Dokar ZabeelectionsElectoral ActFestus OkoyeHukumar Zabe ta KasaINECNational AssemblyOluwatoyin BabalolaTagMajalisar TarayyaYiaga Africazabe
Previous Post

Bayan shahara a Kannywood, ina so in zama babbar ‘yar kasuwa – Sadiya Sareena

Next Post

Takarar 2023: An maida Ali Nuhu gwamnan Kogi

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Ali Nuhu ya hakimce a ofis a matsayin Gwamna Yahaya Bello

Takarar 2023: An maida Ali Nuhu gwamnan Kogi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!