ƊIMBIN mata ‘yan fim sun taya ‘yar’uwar su Rahama Isah (‘Sirace’) murnar haihuwar da ta yi.
Rahama ta haifi ‘ya mace ne a ranar 9 ga Disamba, 2019, a Kano.
An raɗa wa jaririyar suna Fatima.
Jarumai matan sun je gidan mijin Rahama ɗin da ke unguwar Kuntau ‘Forestry’, Kano, bayan kwana biyu da haihuwar, wato ranar 11 ga wata, inda su ka yi mata barka.
Matan sun haɗa da Zakiyya Ibrahim, Fauziyya Sani (‘Maikyau’), Siddiqa Jibrin Sarki, Samira Ahmad, Fati Al-Amin, Jamila Gamdare da Hafsat Iliyasu.

Wata majiya ta shaida wa mujallar Fim cewa mijin Rahama ɗin ya ce ba ya so a yi taron suna, shi ya sa ba a yi wata walima ba.
Idan kun tuna, mujallar Fim ta taɓa ba ku labarin cewa an ɗaura wa Rahama Sirace aure ne da wani mai suna Abubakar Adamu Bala, a unguwar Ja’en cikin garin Kano, a ranar Juma’a, 27 ga Afrilu, 2018. Sadakin ta N50,000.
Ta na daga cikin jarumai mata da su ka daɗe a Kannywood ba su yi aure ba.
Wannan ita ce haihuwar ta ta biyu. A auren ta na farko, wanda ta yi a jihar su ta Borno, ta samu ɗa namiji.
To Allah ya raya su baki ɗaya, amin.


