• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Har yanzu na ɗauki kai na a mawaƙi, inji jarumi Auwal Ishaq (Yawale Ɗankurma)

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
October 22, 2022
in Mawaƙa
0
Auwal Ishaq: "Idan ana gadon waƙa, na gaje ta"

Auwal Ishaq: "Idan ana gadon waƙa, na gaje ta"

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

AUWAL Ishaq, jarumin Kannywood wanda ake kira Yawale Ɗankurma a shirin dirama na ‘Kwana Casa’in’, ya bayyana cewa duk da yake ya shahara a fagen aktin, har yanzu ya na kallon kan sa ne a matsayin mawaƙi.

A tattaunawar da ya yi da mujallar Fim, Auwal, wanda asali mawaƙi ne, ya yi nuni da cewa ya samu shahara a fim tun daga lokacin da ya fara fitowa a cikin finafinan Adam A. Zango, wanda shi ne ya fara saka shi a fim. Idan aka samu rol na barkwanci sai a saka shi. 

Ya ce daga baya ne ya samu shiga shirin ‘Kwana Casa’in’ inda ya ke fitowa a matsayin Yawale Ɗankurma.

Ya ce: “Amma gaskiya duk da sunan da na yi a cikin shirin ‘Kwana Casa’in’, a yanzu na fi ɗaukar kai na a matsayin mawaƙi.”

To me ya sa haka? Auwal ya ce: “Shi fim sa kai ne, saboda ni duk abin da na sa kai na zan yi sai ka ga Allah ya taimake ni na yi nasara. Shi ya sa ma ko da na fara aktin ban ji cewa ba zan iya ba.”

Ya ci gaba da cewa, “Amma ita harkar waƙa zan iya cewa na gada ne, domin mahaifi na makaɗi ne. Don haka idan ana gadon waƙa, to ni na gaje ta ne a wajen mahaifi na.”

Da mu ka tambaye shi game da ɗaukakar da ya samu kuwa cewa ya yi: “Ai harkar fim ta fi ɗaukaka ni, musamman a shirin ‘Kwana Casa’in’. Duk inda na je zan ji ana ga Yawale Ɗankurma ko a ce saurayin Rayya. Kuma a dalilin sunan da na yi a harkar fim na je ƙasashen Kamaru da Chadi da Ghana da Nijar, da kuma manyan garuruwan ƙasar nan. To alhamdu lillahi, mu na godiya ga Allah. 

“Kuma mu na fatan ɗaukakar da mu ka samu ta kai mu ga gamawa lafiya.”

To, amin Auwal.

Loading

Tags: Adam A. ZangoArewa 24Auwal IshaqbarkwancigadojarumimawaƙiRayyaShaharaYawale Ɗankurma
Previous Post

Ban taɓa yin sana’ar shayi ba – Ɗantani Maishayi

Next Post

Buhari ya karrama Minista Sadiya da kyautar inganci da sadaukarwa a aiki

Related Posts

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi
Mawaƙa

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

April 19, 2025
Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala

October 28, 2024
Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala

July 16, 2024
Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara
Mawaƙa

Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara

May 13, 2024
Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 
Mawaƙa

Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 

December 7, 2023
Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala
Mawaƙa

Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala

December 3, 2023
Next Post
Shugaban Ƙasa Buhari ya na miƙa kyautar karramawa ta ingancin aiki ga Hajiya Sadiya Umar Farouq

Buhari ya karrama Minista Sadiya da kyautar inganci da sadaukarwa a aiki

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!