• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Harkar fim a yanzu mun yi girman da za mu bar wa yara – Lilisco

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 2, 2022
in Labarai
0
Idris Shu'aibu Lilisco: An manyanta

Idris Shu'aibu Lilisco: An manyanta

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN jarumin Kannywood Shu’aibu Idris (Lilisco) ya bayyana cewa shi a yanzu harkar fim ya bar wa na baya, sai dai ya riƙa fitowa a matsayin manya kuma ya zamo mai bada shawara ga matasa masu tasowa.

Lilisco, wanda ya ƙware a wajen koyar da rawa kafin ya ƙara haske a fagen fitowa a matsayin jarumi, ya bayyana hakan ne a lokacin wata tattaunawa da mujallar Fim ta yi da shi a matsayin sa na tsohon ɗan wasa da ya jima ana damawa da shi a cikin harkar.

Ya ce, “To mu a yanzu sai dai mu yi godiya ga Allah da ya sa mu ka samu kan mu a wannan lokacin da wasu abubuwa sai dai mu ga ana yi. Domin kuwa a baya mu ake kallo, kuma wasu abubuwan ma idan ba mu ne mu ka yi ba, to ba zai yiwu ba.

Ya ƙara da cewa: “A a wancan lokacin ka ga idan ana maganar rawa ta zamani da ta gargajiya, ai mu ne masu yi kuma mu ne masu koyar da ita. Shi ya sa a lokacin mu ake kallo, mu ne jaruman. 

“Amma a yanzu fa? Wasu ake yayi, su ne su ke cin lokacin su. To, ka ga kowa da lokacin sa. Don haka a yanzu ko da za mu fito a fim sai dai a matsayin iyaye ko wani rol ɗin da ya dace da babban mutum, shi ya sa za ka ga a finafinan da na ke fitowa a yanzu na fi fitowa a jami’in tsaro ko wani ma’aikacin ofis.”

Dangane da yadda harkar fim ta ke a yanzu kuwa wajen rashin tsari, jaruɓin ya ce, “Ai duk wannan abin yawa ne ya jawo hakan, domin a wancan lokacin ba mu da yawa, sai ka ga idan darakta biyu su na aiki to sun ɗebe jaruman masana’antar da sauran masu aiki, sai ka ga babu kowa. Amma a yanzu idan darakta ashirin su na aiki lokaci guda idan ka zo sai ka ga kamar ma wasu ba su tafi aiki ba.

“To, don haka an yi yawa, dole a samu rashin tsari. Wannan kuma ya sa aka samu raunin shugabanci.”

A kan batun makomar harkar fim kuwa, Lilisco ya ce, “Makomar ta mai kyau ce ga wanda ya yi abu mai kyau, domin saboda mun yi abu mai kyau shi ya sa mu ka kawo har yanzu ana damawa da mu. 

“A yanzu ga shi mun yi aure mun yi ‘ya’ya duk a cikin harkar fim ɗin. Don haka fatan mu sai dai Allah ya ba mu cikawa da imani, Allah ya raya zuriyar mu, ya kyautata bayan mu.”

Loading

Tags: Idris Shu'aibu LiliscojarumaiKannywoodLiliscomatasarawa
Previous Post

Abin da ya sa na shirya taron addu’a ga ƙasa – Rarara

Next Post

Baban mu Shehu Ɗahiru Bauchi ya cika shekara 98

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi

Baban mu Shehu Ɗahiru Bauchi ya cika shekara 98

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!