DUBI waɗannan hotunan. Yanzu saboda Allah waɗannan ‘yanmatan sun yi kama da mawaƙan Hausa!?
Ko dai su mawaƙan da daraktocin da su ke bai wa waɗannan ‘yanmatan irin waɗannan suturun da sunan waƙar Hausa ba su da mafaɗa ne? Ko dai su na da wata manufa ne?
Abu wasa wasa sai daɗa haɓaka ya ke. In su na son su waƙoƙin Turanci, su nemo Turawa su yi musu rawa; ba wanda ya ce kar su yi, amma akwai wulaƙanci da rainin hankali a cusa yarinya a cikin tsukakkun kaya a sa ta rawa da su, wai kuma waƙar Hausa, kowa kuma ya zuba ido ya na kallo.

A duk lokacin fa da mutum ya rasa al’adar sa, to ya rasa ta, an gama cin sa da yaƙi, ya zama hoto.
Ya kamata waɗannan mawaƙa su yi wa kan su faɗa. Ba abin da zai hana su bai wa waɗannan ‘yanmatan kayan Hausawa su sa in ya zama dole sai sun yi rawa da waƙa da su.
Ba wani burgewa ba ne a sa kayan Turawa. Mayar da kai baya ne. Saboda ko Turai ka je da kayan ka na gida sai ka fi burge su, sai ka ga su na tsayawa su na ma magana. Amma ka sa nasu ko kallo ba ka ishe su ba.
Shi ya sa da na ga su Rahama Sadau wai an je Amerika an sa ƙananan kaya har da ƙona gashi na ce kash!, waɗannan sun kwafsa. Allah Ya kyauta.
Dakta Maryam Ali Ali malama ce a Sa’adatu Rimi College of Education, Kumbotso, Kano

Allah sarki Dr Maryam ai sai dai ire iren mu muyi ta sharhi amma ba abun da zai canja,ai babban laifin duk na hukuma ne, in duniya da gaskiya su directors da producers su saka kannen su mata mana a roll din, amma dayake kudi suke nema, su kuma ‘yan matan duniya na rudunsu ga mafiya yawansu ba tarbiya daga ganin su fitsara ta mamaye su tun daga gidan da suka fito, illah akwai lokacin da ba za ayi ba. Yanzu ai yayin album ne yazo saboda ba rawan da wakan a finafinai, shiyasa kasuwan su yake ci. Yau ina ‘yan copyn Indian film sun gama kasuwan su, ba don sun so ba sai don zamani yazo mana da drama series, a shekarun baya da Rabiu Bebeji Allah jikan sa da Prof. Abdallah Uba suke sharhi kan illar copyn India a mayar dashi Hausa films, ai producer’s din cewa suka yi hassada ake musu don an ga suna samun kasuwa(to yau su samu, aiga ‘yar manuniya ta nuna).Ina jinjina wa uban tafiya Malam Sheme, da producers Ahmad Bifa da shirin sa na ZAMAN AURE,Falalu Dorayi da shirin sa na GIDAN BADAMASI, Aminu Saira, Nazir Sarkin Waka, Nazifi Asnanic da shirin su na LABARINA,Ibrahim Birniwa da shirin sa na SIRRIN BOYE, sai Lawan Ahmad da Nura Mustapha Waye da shirin su na IZZAR SO. Allah qara daukaka da basira