• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Idris ya ƙaddamar da shugabannin hukumar gudanarwar NIPR, ya jaddada aiki tare domin cimma nasarar Ajandar Sabon Ƙudiri

by WAKILIN MU
January 17, 2024
in Nijeriya
0
Idris ya ƙaddamar da shugabannin hukumar gudanarwar NIPR, ya jaddada aiki tare domin cimma nasarar Ajandar Sabon Ƙudiri

Minista, Mohamed Idris, ya na rantsar da shugabannin NIPR

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada tabbacin yin aiki tare da Cibiyar Ƙwararru Kan Hulɗa Da Jama’a Da Yaɗa Labarai (NIPR) wajen tsare-tsaren hanyoyin sadarwar da za su tabbatar da cimma nasarar Ajandar Sabon Ƙudiri ta gwamnatin Tinubu.

Idris ya yi wannan tabbaci ne lokacin da ya ke jawabi a wurin rantsar da mambobin Hukumar Gudanarwar NIPR a ranar Talata a Abuja.

Wannan bayani ya na ƙunshe a cikin sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na Minista, Rabi’u Ibrahim ya fitar a ranar Talata.

Idris ya ce: “A matsayi na na ɗan wannan cibiyar, na fahimci muhimmancin kare martaba da ƙima. To kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai ta ƙudirta yin aiki tare da wannan cibiya domin shata tsare-tsaren sadarwa da yaɗa labarai, waɗanda za su zaburar da Ajandar Sabon Ƙudiri ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Tilas in bayyana maku cewa na yi matuƙar gamsuwa da irin tsare-tsaren da majalisar NIPR ta fito da su, a ƙarƙashin Dakta Ike Neliaku, kamar yadda aka nuna min kafin fara wannan taron.

“Ina da yaƙinin cewa matuƙar aka aiwatar da waɗannan tsare-tsare, to duk su na da karsashin da za su ɗabbaƙa wannan cibiya, kuma su ɗaukaka wannan ƙasa a idon duniya.”

Mohammed Idris na gabatar da jawabi

Ministan ya ɗora wa cibiyar nauyin sake farfaɗo da ƙima da martabar Nijeriya a duniya, ya ce darajar kowace ƙasa ita ce tushe ko ginshiƙin gina ƙasar.

Ya ƙara da cewa daga cikin ƙalubalen da Nijeriya ke fuskanta, akwai abin da ya kira rashin ɗaukar ‘yan ƙasar da ita kan ta ƙasa da wata ƙima. Wannan kuma a cewar sa ba komai ya janyo hakan ba sai mummunar fassara da bahaguwar fahimtar da ake mana a faɗin duniya.

Ya ce: “Wannan kuma abu ne mai ɓacin rai a matsayin mu na ƙwararru. Don haka tilas mu bijiro da hanyoyin da za su kasance mafita, waɗanda za mu nuna wa duniya irin baiwa, daraja, ƙima da martabar da wannan ƙasaitacciyar ƙasa Nijeriya ke da ita.

“Sauran ƙasashe ma kowace na da nata matsalolin, amma inda bambancin yake shi ne ta yadda su ke tunkarar daƙile wani aibi.
“Wannan kuwa abu ne da ake iya cimma nasarar sa ta hanyar haɗa kai tsakanin gwamnati da ƙwararru irin NIPR da kuma kishin ‘yan ƙasa.”

Daga nan ya jinjina wa nagartattun mutanen da su ka kafa cibiyar shekaru 60 da su ka gabata, ta yadda yanzu har ta na ɗaya daga cikin cibiyoyin ƙwararru ƙalilan da ake da su a duniya, waɗanda gwamnati ta yi amanna da su ɗari bisa ɗari.

Wasu mahalartan taron

Loading

Tags: Alhaji Mohammed Idris MalagiNIPR
Previous Post

Tinubu ya naɗa Mohammed Idris cikin kwamitin yi wa Shirin Inganta Rayuwar Masara Galihu garambawul

Next Post

Cika shekara 60: Buri na a rayuwa ya cika – Ado Ahmad Gidan Dabino

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Cika shekara 60: Buri na a rayuwa ya cika – Ado Ahmad Gidan Dabino

Cika shekara 60: Buri na a rayuwa ya cika - Ado Ahmad Gidan Dabino

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!