A CIKIN farkon wannan watan ne aka kammala aikin wani sabon fim mai suna ‘Igiyar Ƙasa’, wanda furodusa Saminu S. Turaki da ke garin Maraɗi ta Jamhuriyar Nijar ya shirya.
Fitacciyar jaruma a ƙasar Nijar, Maimounatu Ibrahim Nagari, wadda aka fi sani da Mamy Pullo, ita ce ta fito a matsayin jarumar shirin.
Ganin irin rawar da ta taka a lokacin ɗaukar fim ɗin, mujallar Fim ta nemi jin ta bakin ta don jin tarihin fim da kuma burin ta a harkar fim a Nijar, kamar haka:
FIM: Ki gabatar da kan ki ga masu karatun mu.
MAMY PULLO: Ni dai suna na Maimounatu Ibrahim Nagari, wadda aka fi sani da Mamy Pullo. Kuma na fito a matsayin Dije a cikin fim ɗin ‘Igiyar Ƙasa’.
Ni an haife ni a Maraɗi ta Jamhuriyar Nijar a 12/12/1998. Sannan na fara karutu a 2006, kuma na fara fim ne a 2013 duk da cewar ba wai harkar fim na tsaya ba domin ina yin waƙa; ka san a Nijar waƙa aka fi yi, don haka na yi finafinai da yawa da kuma waƙa. Ba wannan ba ne fim ɗin da na fara yi.

FIM: Kin daɗe ki na yin fim. Me ya bambanta wannan da sauran waɗanda ki ka yi?
MAMY PULLO: Gaskiya na ji daɗin aikin wannan fim ba kamar na baya ba da na ke yi, don haka na ji daɗin kasancewa ta a cikin sa. Sannan a halin yanzu Ina tsakanin ‘yan kallo masu yabo da masu kushewa duk ina sauraron su.
FIM: Wanne buri ki ke da shi a yanzu?
MAMY PULLO: To, babban buri na dai shi ne na yi abin da zai fito da ƙasar mu ta Nijar a duniya ta zama ta na cikin ƙasashen da su ke yin fim masu tashe a duniya, don ina son ƙasar mu ta ci gaba, Allah ya kawo mana cigaban wannan harkar ta fim a Nijar. Kuma ina fatan Allah ya kawo mini miji na yi aure.

![]()







