• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

INEC ba ta nuƙu-nuƙu da kayan zaɓe, za mu bai wa masu shigar da ƙara bayanan da kotu ta ce a ba su – Yakubu

by DAGA WAKILIN MU
March 15, 2023
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu

Farfesa Mahmood Yakubu

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa a shirye ta ke ta damƙa kwafen bayanai da dukkan kayan da kotu ta bayar da umarni ga jam’iyyu ko ‘yan takarar da ke ƙorafi kan zaɓen ranar 25 ga Fabrairu, domin su yi nazarin da su ke so su yi.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya karɓi tawagar lauyoyin jam’iyyar  Labour (LP), bisa jagorancin Babban Lauya Livy Uzoukwu.

Tawagar lauyoyin dai ta ziyarci hedikwatar INEC ne a ranar Litinin a Abuja.

Yakubu ya tabbatar masu da cewa ya karɓi wasiƙar da LP ta aika masa a ranar 6 ga Maris, wadda ta sanar da shi cewa lauyoyin ta za su kai ziyara INEC domin duba kayan zaɓe.

Ya ce wasiƙar na ɗauke da ƙarin bayanin sanar da shi cewa ya sanar da Kwamishinonin Zaɓe na INEC da ke a kowace jiha, cikin jihohi 36 na faɗin ƙasar nan da Abuja.

Wasiƙar dai ta nemi INEC ta umarci Kwamishinonin Zaɓe na jihohin su damƙa wa LP bayanai da kayan da ta ke buƙata domin gabatar da bayanan ƙarar ta a kotu.

Yakubu ya ce INEC ta shirya gudanar da taro da Kwamishinonin Zaɓe, domin su tattauna batutuwa da dama, ciki har da batun bayar da sahihan kwafe-kwafe na bayanan zaɓe ga dukkan waɗanda su ka shigar da ƙara, ba ma ga LP ita kaɗai ba.

“Ina tabbatar maku da cewa INEC ba ta wani nuƙu-nuƙun ɓoye komai. Za mu ba ku dukkan abin da ku ke buƙata.

“Kwafen bayanai biyu ne ke a hannun Hedikwatar INEC nan a Abuja. Kuma za mu iya samar maku waɗannan kwafen ba tare da  ɓata lokaci ba. Akwai kwafen sakamako na EC8Ds da aka tattara daga jihohi da kuma mai lamba EC8DA, wanda sakamakon zaɓe ne da INEC da kan ta ta tattaro daga cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.

“Mai lamba EC8DA dai ina jin kwafe 39 ne. Kuma za mu iya samar maku kwafen su ba tare da ɓata lokaci ba,” inji Yakubu.

Ya ce sauran kwafen bayanai kuma duk su na ofisoshin INEC na jihohi daban-daban, kuma hukumar za ta so sanin ranakun da lauyoyin za su je jihohi domin a shirya masu kwafen kafin su isa, yadda su na zuwa sai dai su fara nazari kawai’.

“Sauran bayanai kuma alƙaluma ne lambobi da bayanan tantance mai shaidar katin rajistar zaɓe na rumfunan zaɓe fiye da 176,000.

“Za mu samu lokaci mu buga kwafe-kwafen su a wadace, sannan mu damƙa maku cikin hanzari.”

Daga nan ya shawarci tawagar lauyoyin INEC su gana da lauyoyin INEC domin su bayyana wa juna batutuwa da dama.

Jagoran tawagar lauyoyin LP, Uzoukwu ya shaida wa Yakubu cewa dalilin ziyarar shi ne domin su share hanyar fara nazarin kayan zaɓen shugaban ƙasa. “Saboda ka san dai mu na da kwanaki 21, waɗanda a cikin su ne za mu shigar da ƙara, a madadin waɗanda mu ke karewa. Yanzu kuma daga cikin kwanaki 21 ɗin, kusan kwanaki 10 kaɗai ne su ka rage mana. Ga shi kuma har yau ɗin nan ba mu karɓi kwafen takardun bayanai ko kayan zaɓe ko da guda ɗaya ba.”

Loading

Tags: INECkotuLabour PartyLivy UzoukwuLPmahmood yakubuZaɓen 2023
Previous Post

Dakan-ɗaka-shiƙar-ɗaka: An saka ranar auren darakta Kamal Alƙali da jaruma Hauwa SG

Next Post

Tallar ‘yan takara: Mun gama shan wahala an yi watsi da mu, inji Fati Nijar

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Fati Nijar: An ci moriyar ganga ne?

Tallar 'yan takara: Mun gama shan wahala an yi watsi da mu, inji Fati Nijar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!