• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, May 15, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

INEC ta gayyaci ‘yan takarar shugaban ƙasa zuwa taron sa-hannun amincewa a gudanar da zaɓe cikin lumana

by DAGA WAKILIN MU
February 19, 2023
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu ya na duba babban zauren Cibiyar Taro ta Duniya (ICC)

Farfesa Mahmood Yakubu ya na duba babban zauren Cibiyar Taro ta Duniya (ICC)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAN Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce dukkan ‘yan takarar shugaban ƙasa za su bayyana a ranar Laraba, domin su sa hannu kan yarjejeniyar amincewar yarda a gudanar da zaɓe lami lafiya, ba tare da tashin hankali ba.

Yakubu ya bayyana haka a lokacin ganawar sa da ‘yan jarida, bayan ya kai ziyara Makarantar Sakandire ta Garki, Abuja, inda ake bayar da horo ga Masu Sa-ido Kan Jami’an Zaɓe (SPO).

Shugaban na INEC ya kuma kai irin wannan ziyarar a Cibiyar Taro ta Duniya (ICC), inda ya ce a can ne jihohi za su riƙa aikawa da sakamakon zaɓe ana tattarawa. Daga ƙarshe kuma a can ne shugaban na INEC zai bayyana ɗan takarar da ya yi nasara, tare da sakamakon da kowane ɗan takara ya samu.

Yakubu ya ce haka kuma ICC za ta kasance Cibiyar Yaɗa Labarai.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, tare da Mataimakiyar Sakataren Harkokin Ƙasashen Ketare ta Amurka mai kula da Al’amuran Afrika, Molly Phee, da Jakadiyar Amurka a Nijeriya, Mary Beth Leonard, lokacin ziyarar su a hedikwatar INEC don tattauna batun zaɓen 2023

Haka kuma Yakubu ya ce INEC ba za ta fuskanci matsalar ƙarancin kuɗi ba, bisa dogaro da alƙawarin da Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya yi wa shugaban na INEC, a lokacin da ya ziyarce shi.

Ya ce yawancin ayyukan da INEC za ta biya ma’aikata duk tura masu a asusun ajiyar su za ta yi.

Da ya ke magana kan ƙalubalen tsaro, ya ce wannan aikin jami’an tsaron ƙasa ne, kuma sun yi alkawarin babu wani gagararren da za’a bari ya haifar wa zaɓen 2023 da cikas.

Ya ce Kwamitin Wanzar da Zaman Lafiya na Ƙasa da ke ƙarƙashin tsohon  Shugaban Ƙasa, Janar Abdulsalami Abubakar (ritaya), shi ne zai shirya taron rattaba hannun amincewar da ‘yan takarar za su yi a ranar Laraba, 22 ga Fabrairu, 2023, a ICC a Abuja.

Ya ce INEC ta kammala shirye-shiryen gudanar da zaɓen 2023 a cikin kwanciyar hankali.

Loading

Tags: 'yan jaridaBVASCBNICCINECmahmood yakubuUS Embassy AbujaZaɓen 2023
Previous Post

Maishadda ya yi raddi ga masu tsegumi kan ziyarar gidan Halima Atete da su ka yi

Next Post

Matasan NYSC kaɗai INEC ta amince su yi aiki da na’urar tantance masu katin rajista – Yakubu

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Farfesa Mahmood Yakubu ya na jawabi lokacin da shugabannin INEC su ka kai ziyara a cibiyar horas da jami'an zaɓe a GSS Garki, Abuja

Matasan NYSC kaɗai INEC ta amince su yi aiki da na'urar tantance masu katin rajista - Yakubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!