• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 9, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Jamila Kogi: Yadda mu ka tsallake rijiya da baya

by DAGA ABBA MUHAMMAD
December 5, 2020
in Labarai
0
Jamila Kogi na nuna raunukan da ta ji a hannayen ta; a sama kuma motar da ta faɗi da su ce

Jamila Kogi na nuna raunukan da ta ji a hannayen ta; a sama kuma motar da ta faɗi da su ce

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
SUBHANALLAH! Fitacciyar mawaƙiyar nan da ke Kaduna, Jamila Muhammad, wadda aka fi sani da Jamila Kogi, ta tsallake rijiya da ƙundun baya ita da wasu abokan sana’ar ta ‘yan garin su a kan hanyar su ta komawa Jihar Kogi daga garin Lafiya a Jihar Nassarawa.
 
Wannan mummunan al’amari ya faru ne a safiyar jiya Juma’a da misalin ƙarfe 11:00, inda motar da su ka shigo ta yi ƙundunbala da su, sanadiyyar wata babbar mota. 
 
Jamila ta yi wa mujallar Fim cikakken bayanin yadda al’amarin ya faru kamar haka:
 
“Assalamu alaikum! Abin da ya faru, mu na bayan wata babbar mota ne, sai wata mota ta taho a guje. 
 
“Shi mai babbar motar ya na ƙoƙarin taka birki, motar kuma idan direban ya ce zai taka birki za mu shige ƙarƙashin wannan babbar motar, sannan kuma ga wasu motoci biyu su ma su na ƙoƙarin kaucewa, mu kuma sai direban mu ya kauce.
 
“Nan ma kaɗan ya rage mu haɗa jiki da waccan motar, kaucewar da ya yi sai motar mu ta juya, mu ka faɗa rami, tayoyin sun koma sama, saman motar na ƙasa. 
 
“Cikin ikon Allah, mu ka samu mu ka fita ta tagar motar.
 
“Babban abin godiya ga Allah, ba a samu rasa rai a ciki ba. Kuma da ma dukkan mu ‘celebrities’ ne na can garin mu a cikin motar: ni, Abdul, MC Bash, Halima KD, sai wata Hauwa da Blincks. 
 
“Mun taso daga Lafiya za mu tafi Kogi, an gama bikin da mu ka je. Wannan abu Allah ya kiyaye, don mun ɗauka ma ba za mu rayu ba, gaskiya. 
 
“Kuma mun gode wa Allah don babu wanda ya ji ciwo sosai, sai ni ce ma na ɗan sassamu raunuka sanadiyyar farfashewar da gilas ya yi. Sauran ba su samu rauni ba, sai dai gajiya. 
 
“Shi Blinks ne ma mu mun fita, shi ya kasa fita, sai da mu ka yi ta kiran sa mu na gudun kada motar ta kama da wuta, domin man motar ya na ta wari. Da ƙyar ya samu ya fito. 
 
“Kuma shi mai motar da ya ja mana haɗarin bai ma tsaya ba, tafiyar sa ya yi.
 
“Babban tashin hankali, a wurin babu ‘network’ ɗin waya. Don ko waya ta sai da alam ɗin ta ya buga sannan na gano inda wayar ta ke. 
 
“Daga nan aka kwashe mu aka kai mu asibiti a can Lafiya. Amma yanzu an sallame mu. 
 
“Mu na buƙatar addu’ar masoya da ‘yan’uwa da abokan arziki. 
 
“Duk wanda ya zo wurin sai ya yi mamakin yadda aka yi mu ka fi lafiya a cikin motar, don sai da mutane su ka zo sannan aka juya motar kamar yadda ka gan ta a hoto. 
 
“Kuma inda Allah ya taimake mu dukkan mu babu mai ihu, sai salati kawai mu ke yi. Allah kuma ya kiyaye, ba don direban mu ya kauce ba, za mu yi gaba da gaba ne da waccan motar.”
 
To Jamila, mu na fatan Allah ya kiyaye gaba. Allah kuma ya ba ki lafiya.

Loading

Previous Post

Aure: Nuhu Abdullahi da Siyama sun zama ɗaya

Next Post

Shekara 60 a Kannywood: Rayuwar Ladin Cima (Tambaya) a yau

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Tambaya a lokacin tattaunawar ta da mujallar Fim

Shekara 60 a Kannywood: Rayuwar Ladin Cima (Tambaya) a yau

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!