Komai ya na da lokacin sa. Jamilu Sa’eed Ɗanmasukuɗi ya na ɗaya daga cikin mawaƙan da ake zolaya da cewa ba su yi aure ba.
To, yau dai Allah mai kowa mai komai ya wanke shi, inda ya haɗa shi da sahibar sa, Maryam Umar.
Tun ana kusan saura mako biyu a ɗaura auren, Jamilun ya fara yaɗa hotunan sa tare da amaryar tasa a soshiyal midiya, inda ya riƙa tunatar da ’yan’uwa da abokan arziki cewa bikin su ya matso.
An ɗaura auren a ranar 10 ga Disamba, 2016, a garin Igabi da ke Jihar Kaduna, da misalin ƙarfe 2:00 na rana, a kan sadaki N60,000.
Wasu daga cikin iyayen gidan angon da kuma ’yan fim da su ka halarci ɗaurin auren sun haɗa da Alhaji Amadu Inuwa, El-Mu’az Birniwa, Hajiya Fatima Lamaj, Sani Amalo, Khalid Lamaj, da Mudassir Barumi.
Bayan ɗaurin auren, an shirya gagarumin biki da aka yi wa laƙabi da Ranar Mawaƙa a wani ɗakin taro da ke wurin shaƙatawa na Habil Swimming Pool da ke Titin Muhammadu Buhari a cikin garin Kaduna. An fara bikin da misalin ƙarfe 7:00 na dare. Mawaƙa sun baje kolin su a wurin bikin.
Wasu daga cikin waɗanda su ka halarta sun haɗa da A’isha Tsamiya, Sadiqu Artise, Umar Ɗanhausa, Musa Mairabo, El-Mu’az Birniwa, Ado Ahmad Gidan Dabino, Fa’iza Badawa, Mudassiru Barumi, A’isha ZIAU, Fatima Lamaj, Sagir Baban Kausar, Sani Chairman, Adam A. Zango, Kabiru A. Zango, da Musa A.A. Rasheed.
An tashi daga bikin da misalin ƙarfe 10:00 na dare.
Allah Ya ba ango da amarya zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.