JARUMIN Kannywood, Abdullahi Amdaz, wanda aka fi sani da Excellency shi ma dai ya yi shirin zama mai igiya biyu kafin shekarar nan ta ƙare. Wato zai ƙara aure.
Amdaz zai angwance da sahibar sa, A’isha Umar Timta, a ranar Asabar, 30 ga Disamba, 2023.
Za a ɗaura auren da misalin ƙarfe 11:00 na safe a gidan Sarkin Gwoza da ke Titin Gombale, kusa da makarantar Capital, Giwa Barrack, Maiduguri, Jihar Barno.

A katin gayyatar da mujallar Fim ta samu, jarumin ya buƙaci addu’a a wurin masoyan sa da ‘yan’uwa da abokan arziki.