• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Kotu ta hana beli ga matasan da ake zargi da yin zamba da ɓatanci da sunan Iman Sani Danja

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
September 20, 2022
in Labarai
1
Hajiya Mansurah Isah da Khadijatul Iman Sani Danja

Hajiya Mansurah Isah da Khadijatul Iman Sani Danja

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

KOTUN Majistare mai lamba 47 da ke Kano a jiya ta ƙi ba da beli ga wasu matasa biyu da aka kama bisa zargin su na amfani da sunan jarumar Kannywood Khadijatul Iman Sani Danja su na zambatar jama’a tare da yaɗa batsa a soshiyal midiya.

A jiya Litinin ne dai aka sake gabatar da Jabir Muhammad da Abubakar Sunusi a gaban Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan bisa tuhumar haɗa kai da ƙirƙirar labarin ƙarya da cin zarafi da kuma ɓata suna.

Jami’in kotun, Auwal Abdullahi, ya karanto masu laifin su tare da bayyana cewa abin da su ka yi ya saɓa wa sashe na 97 da na 324 da na 393 da kuma na 392 na kundin Final Kod.

To amma dukkan su sun musanta zargin.

Lauyar gwamnati mai gabatar da ƙara, Barista Asma’u T. Gwarzo, ta buƙaci kotu da ta ba su wata ranar domin a sake gabatar da su, kuma a nan take kotun ta amince, inda ta aika da su zuwa gidan yari inda za su zauna har zuwa ranar 27 ga Satumba, 2022 sannan a sake gabatar da su.

Mahaifiyar Iman, wadda ƙaramar yarinya ce, wato tsohuwar jaruma Hajiya Mansurah Isah, ita ce ta kai su ƙara a madadin ‘yar ta.

Uwa da ‘ya: Mansurah da Iman

Bayan an fito daga kotun, mujallar Fim ta tattauna da lauyan Mansurah ɗin, wato Barista Rabi’u Sidi, inda ya bayyana dalilin shari’ar da kuma inda aka tsaya. Ya ce, “Ni ina tsaya wa Mansurah Isah ne a kan wannan ƙara inda mu ke ƙarar wasu mutane uku, Jabir Muhammad, Abubakar Sunusi, da kuma wani da har yanzu ba a kai ga kama shi ba, dangane da haɗa kai da su ka yi wajen buɗe shafuka na Facebook, Instagram, Twitter da YouTube inda su ka kira shafin da suna ‘Real Iman Sani Danja’ su na saka hotunan batsa, sannan su ka yi amfani da lambobin wayar su su na kiran wasu mutane su na karɓar kuɗaɗe a wajen su a matsayin ita ce. 

“Kuma sai binciken ya nuna an yi wannan abin domin ɓata wa ita Mansurah Isah suna da iyalan ta. Don haka sai ta gabatar da ƙorafi a gaban ‘yan sanda na SIB kuma aka yi bincike aka kamo su.

“A yanzu ga shi an gabatar da su a gaban kotu, duk da cewa sun musa abubuwan da aka caje su da shi Lauyan su ya tashi ya nemi beli a gaban kotu, ta ce ta ɗaga sai ranar 27 za ta faɗi ra’ayin ta ko za ta bayar da belin ko ba za ta bayar ba.

“Don haka mu dai abin da mu ke nema ga kotu ta yi mana adalci a kan wannan shari’ar, domin akwai mutane da dama da su ke amfani da shafuka na manyan mutane su na ɓata musu suna tare da karɓar kuɗaɗe a wajen wasu da sunan su, don haka mu ke so kotu ta yi hukunci don ya zama izna ga wasu.”

Loading

Tags: Abubakar SunusiBarista Asma'u T. Gwarzo.Barista Rabi'u Sidi.ɓatancifake newsFinal KodJabir MuhammadKhadijatul Iman Sani DanjakotuMai Shari'a Hadiza Muhammad Hassan.majistareMansurah Isahremandzamba
Previous Post

Umar Bankaura ya buƙaci addu’ar jama’a saboda matsanancin rashin lafiya da ya ke fama da shi

Next Post

Lamaj ta ƙaryata Sha’ani kan rashin kuɗi a asusun MOPPAN ta Kaduna

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Hajiya Fatima Ibrahim (Lamaj)

Lamaj ta ƙaryata Sha'ani kan rashin kuɗi a asusun MOPPAN ta Kaduna

Comments 1

  1. Pingback: Kotu ta hana beli ga matasan da ake zargi da yin zamba da ɓatanci da sunan Iman Sani Danja - LastNg

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!