• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, June 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mai tallafa wa Kannywood, Farfesa Sule Bello, ya rasu

by DAGA IRO MAMMAN
October 3, 2021
in Labarai
0
Marigayi Farfesa Sule Bello (1953-2021)

Marigayi Farfesa Sule Bello (1953-2021)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAHU Akbar! Allah ya yi wa wani babban mai tallafa wa harkar adabi a Nijeriya, ciki har da harkar finafinan Hausa, rasuwa, wato Farfesa Sule Bello.

Ya rasu a yau Lahadi, 3 ga Oktoba, 2021, bayan gajeren rashin lafiya.

Sule Bello ya rasu a Zariya, ya na da shekaru 73 a duniya. 

Kafin rasuwar sa, babban malami ne a Sashen Tarihi na Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya.

Haka kuma shi ne shugaban wani tsagi na jam’iyyar PRP na ƙasa.

Wata majiya ta ce za a yi jana’izar sa a gidan sa da ke Titin Maiduguri a unguwar Hotoro GRA, a Kano.

Majiyar ta ce kwana ɗaya kafin rasuwar sa, wato jiya, an shirya zai gabatar da wata lacca wadda wata ƙungiyar matasa ta shirya a kan batun samun ‘yancin Nijeriya, a wani taro da aka yi a Kano, to amma saboda ciwon sa ya tashi sai ya tura wakili.

Mujallar Fim ta gano cewa Farfesa Sule Bello ya taimaka wa harkar shirya finafinan Hausa a lokacin da ya ke riƙe da muƙamin Daraktan Hukumar Tarihi da Al’adun Gargajiya ta Jihar Kano (History and Culture Bureau). Kwanan nan ma ƙungiyar dattawan Kannywood ta naɗa shi shugaban kwamitin amintattu na Gidauniyar Kannywood (Kannywood Foundation).

Farfesa Sule Bello ya bada gagarumar gudunmawa a fagen kyautata al’adu, karantarwa, binciken tarihi da kuma gwagwarmayar siyasa a Afrika.

Mutum ne mara tsoro wajen faɗin gaskiya komai ɗacin ta.

An haifi Farfesa Sule Bello a Kano a ranar 5 ga Janairu, 1953. Ya yi karatu a Ƙaramar Makarantar Firamare ta Gidan Makama (1959 – 1962), Kano, da Babbar  Makarantar Firamare ta Rano (1963-1966). Daga nan ya shiga Kwalejin Rumfa, Kano.

Sule ya yi karatun share fage a Jami’ar Ahmadu Bello, wato ABU, Zariya (1971-1972), sannan aka ɗauke shi ya karanta Kimiyyar Siyasa (Political Science) da Tarihi a jami’ar, ya gama a 1975.

An ɗauke shi aikin koyarwa a jami’ar a 1976. Ana cikin haka ya yi karatun digiri na biyu a fannin Tarihi a  nan dai ABU ɗin, wanda wannan digirin ne aka ɗaga aka ba shi digiri na uku (PhD, History) a 1982. Taken kundin digirin sa na uku shi ne ‘State and Economy in Kano’ inda ya yi nazarin tattalin arzikin Kano a zamanin mulkin mallaka.

Farfesa Sule Bello ya ci gaba da koyarwa a Jami’ar Ahmadu Bello (in ban da lokacin da ya je ƙaro karatu a Jami’ar Kent, Canterbury, a Ingila) har zuwa 1987 lokacin da ya zama Daraktan Hukumar Tarihi da Al’adun Gargajiya ta Jihar Kano (History and Culture Bureau, HCB). Daga can kuma aka naɗa shi Daraktan Hukumar Fasaha da Al’adu ta Tarayya (National Council for Arts and Culture), Abuja, muƙamin da ya riƙe har zuwa shekarar 2000. A can ma ya ci gaba da taimaka wa harkar fim da sauran nau’o’i na fasaha da al’adun mutanen Nijeriya.

A cikin Yuni 2006, Sule Bello ya koma Jami’ar Ahmadu Bello domin ci gaba da koyarwa tare da dawo da martabar al’adar binciken tarihi da gabatar da laccoci da aka san Sashen Tarihi da shi a da, musamman a zamanin su marigayi Dakta Yusufu Bala Usman.

A tsakanin 2006 da 2009 ya riƙe muƙamin shugaba (HOD) na Sashen Tarihi na jami’ar. A cikin 2015 kuma ya zama Daraktan Cibiyar Bincike kan Cigaban Ƙasa (Institute of Development Research) ta ABU, sannan aka naɗa shi Daraktan Cibiyar Binciken Tarihi da Adanawa (Centre for Historical Research and Documentation) ta ABU, wurin da aka fi sani da Gidan Arewa ko ‘Arewa House’ da ke Kaduna.

Da ya ƙare, sai ya koma jami’ar ta ABU ya ci gaba da aikin sa na koyarwa. A lokacin ne ya shiga harkar siyasa tsundum, inda ya shiga jam’iyyar PRP, wato ‘Peoples’ Redemption Party’, ya yi cuɗanya sosai da jagoran ta, Alhaji Abdulƙadir Balarabe Musa. 

Mujallar Fim ta gano cewa bayan rasuwar Balarabe Musa, Farfesa Sule Bello ya jagoranci yadda za a farfaɗo da martabar jam’iyyar domin ta sake yin tasiri a fagen zaɓe. A kan hakan, sun yi aiki mai yawa, to amma rikici ya lulluɓe jam’iyyar domin kuwa an tsaga ta gida biyu inda shi Farfesa Sule Bello ya zama shugaban tsagi ɗaya.

Mutuwar Farfesa Sule Bello ta biyo bayan ta wani zaƙaƙurin malamin tarihin a jami’ar ABU, wato Farfesa Ɗahiru Yahya, wanda ya rasu a ranar 3 ga Fabrairu, 2021. Mutane da yawa sun gigita, har ana ganin jami’ar ba ta taɓa ganin rashi da ya girgiza ta ba irin waɗannan rashe-rashe biyu tun lokacin da Dakta Yusufu Bala Usman ya rasu a cikin 2005.

Allah ya jiƙan su baki ɗaya, amin.

Loading

Tags: Abdulkadir Balarabe MusaABU ZariaAhmadu Bello UniversityArewa HouseDr Yusufu Bala UsmanHistoryHotoroHukumar Tarihi da Al'adun Gargajiya ta Jihar KanoJami'ar Ahmadu BelloKannywood FoundationKanoKano State History and Culture BureaumutuwaNational Council for Arts and CulturePeoples Redemption PartyProf Dahiru YahyaProf Sule BelloPRP
Previous Post

Shirin ‘No Time To Die’ na James Bond ya yi cinikin £5m a ranar farko a sinimun Birtaniya

Next Post

Yadda na rasa ‘ya’ya na biyu a cikin motar da na yi fakin – Mawaƙi Sanusi Pambeguwa

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Sanusi Pambeguwa da 'ya'yan sa da su ka rasu: Khaleed (a sama, mara hula) da Tasi'u (Khalifa).

Yadda na rasa 'ya'ya na biyu a cikin motar da na yi fakin - Mawaƙi Sanusi Pambeguwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!