MALAMAN addinin Musulunci da ke Jihar Kano sun bayyana cewa sun tsige shugaban Majalisar Malamai ta jihar, Sheikh Ibrahim Khalil, daga shugabancin majalisar bisa zargin wasu laifuka da su ka yi masa.
A wata sanarwa da Ustaz Saifullahi Adam Assudani da Sheikh Khalifa Gama da Sheikh Abdulƙadir Ramadan da kuma Imam Jamil Abubakar su ka sanya wa hannu, wadda mujallar Fim ta samu kwafe, malaman sun ce sun ɗauki wannan mataki ne da yawun dukkan malaman jihar.
A cewar su, Malam Ibrahim Khalil ya gaza ciyar da majalisar gaba, sannan majalisar ba ta aikin da aka ɗora mata na yin fatawa ga al’umma kan sababbin matsalolin da ke tasowa a wannan zamanin.

Malaman su ka ƙara da zargin sa da yin amfani da ofishin majalisar wajen shirya tarurruka na ƙashin kan sa, ba na majalisar ba, kuma ya gaza haɗe kan ɓangarorin Izala, Ƙadirriyya da Tijjaniya a Kano, sannan kuma ya shiga siyasa har ma takara ya ke nema.
Malaman su ka ce a bisa wannan dalilan ne ya sa dukkan malamai daga ɓangaren Tijjaniya, Ƙadiriyya da Izala su ka ga dacewar su sauke shi daga shugabancin majalisar.
Sai dai sun ce wannan garambawul da su ka yi wa majalisar, shugaban kaɗai ta shafa, sauran shugabannin su na nan a kan muƙaman su.
Daga ƙarshe, sun zaɓi Farfesa Abdullah Saleh Pakistan a matsayin sabon shugaban majalisar, kuma su ka ce kowane ɓangare daga Tijjaniya, Ƙadiriyya da Izala ya amince da wannan matakin.