• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 23, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mansurah na so gwamnati ta sa a riƙa nuna finafinan Hausa a dukkan sinimun Nijeriya

by DAGA IRO MAMMAN
November 8, 2021
in Labarai
0
Mansurah Isah a cikin guntun bidiyon da ta yi magana

Mansurah Isah a cikin guntun bidiyon da ta yi magana

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCIYAR furodusar Kannywood, Hajiya Mansurah Isah, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta fito da wata doka da za ta sa gidajen sinima su riƙa nuna finafinan Hausa a duk faɗin Nijeriya.

Mansurah, wadda tsohuwar jaruma ce, ta bayyana haka ne cikin wani guntun bidiyo mai tsawon sakan 59 da ta wallafa a Instagram a yau.

Furodusar ta bayyana mamaki kan yadda gwamnati ta ke da ikon sa hannu kan yadda ake gudanar da sana’ar sinima a Nijeriya amma ta kasa umartar masu gidajen sinima su riƙa haska finafinan Hausa.

A bayanin da ta yi cikin kakkausar murya, Mansurah ta ce, “Ashe Gwamnatin Tarayya ta na iya saka hannu a harkar sinima a Nijeriya? Ai ni da ban sani ba!

“To mu masu shirya finafinan Hausa wane laifi mu ka yi ne da har za a ce ba za a riƙa haska finafinan mu ba a duk faɗin Nijeriya?”

Furodusar ta yi nuni da cewa gidajen sinima su na nuna finafinan Yarbanci da na Ibo da na Turanci daga kudancin ƙasar nan, na Hausa kaɗai ne ba za su nuna ba.

Ta ce, “To me ya sa mu furodusoshin finafinan Hausa aka bar mu a baya?

“Haba! A taimaka mana mana, a taimaka mana. A yi doka.”

Furodusar ta yi kira ga jami’an hukuma da su fito da dokar da za ta sa gidajen sinima su riƙa nuna finafinan Hausa kamar yadda su ke nuna na ‘yan Nollywood.

Ta ce, “Ku nuna yaren ku, ku nuna al’adar ku. Ku ƙaunace mu. Ku sa finafinan mu a dinga nunawa a duk Najeriya.”

Ta yi nuni da yadda ake kawo fim ɗin Turanci a Kano a dinga haska shi, amma ba za a iya ɗaukar fim ɗin Hausa a kai shi Legas a riƙa nunawa ba. 

“Meye dalili? Me mu ka yi?” inji ta.

Bugu da ƙari, Mansurah ta yi nuni da yadda ‘yan Kannywood su ke mara wa gwamnati baya, amma kuma ita ba ta taimaka masu ta wannan fannin.

Ta ce, “Ba ma zagi, ba ma cin zarafin ku, amma duk da haka mu ne koma-baya.

“Me ku ke so da mu? Na roƙe ku da girman Allah ku taimaka mana.”

Ita dai Mansurah, a makon jiya ta saki sabon fim ɗin ta da ta saki mai suna ‘Fanan’ ya kafa tarihi wajen samun babbar riba irin wadda ba a taɓa gani ba a gidajen kallo na Kano cikin ‘yan shekarun nan.

Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba ku labarin yadda gwamnati ta hana a nuna wani fim ɗin Hollywood mai suna ‘Eternals’ a gidajen sinima na Nijeriya saboda ya na ɗauke da jigon luwaɗi.

A da, an tsara cewa za a fara nuna fim ɗin ne a ranar Juma’a da ta gabata.

Loading

Tags: cinemas in NigeriaFananhausa filmsHollywoodKannywoodMansurah Isahnollywood
Previous Post

Gwamnati ta haramta nuna wani fim kan ‘yan luwaɗi a sinimun Nijeriya

Next Post

Sabon shirin ‘N-Knowledge’ zai horas da matasan Nijeriya 20,000 kan fasahar zamani – Minista Sadiya

Related Posts

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Next Post
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Sabon shirin 'N-Knowledge' zai horas da matasan Nijeriya 20,000 kan fasahar zamani - Minista Sadiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!