• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Masu tattakin Rarara daga Kaduna sun isa Kano

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
September 9, 2022
in Labarai
0
Anas M. Lawan da Mustapha Iliyasu tare da Ayshatulhumaira a ofishin Rarara a ranar Alhamis

Anas M. Lawan da Mustapha Iliyasu tare da Ayshatulhumaira a ofishin Rarara a ranar Alhamis

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MATASAN nan biyu masoyan mawaƙi Dauda Kahutu Rarara da su ka yi tattaki daga Kaduna zuwa Kano sun iso garin a yammacin jiya Alhamis, 8 ga Satumba, 2022.

Mujallar Fim ta ba da labarin yadda matasan, Anas M. Lawan da Mustapha Iliyasu, su ka kama hanya a ƙafa tinkis-tinkis tun daga Kaduna da zummar ganin Rarara a Kano don nuna masa goyon baya kan harkar sa ta siyasa.

Isowar su ke da wuya, su ka nufi ofishin Rarara da ke Titin Gidan Zu.

Sai dai kuma sun daki gurbi ko kuma a ce sun taki rashin sa’a, domin ba su samu ganin masoyin nasu ba saboda ya yi tafiya, ba ya gari.

Amma dai sun samu gagarumar tarba daga wakiliyar sa, fitacciyar jaruma A’ishatu Ahmad Idris (Ayshatulhumaira) wadsa ta tarbe su a madadin sa.

Jarumar ta shirya masu liyafa ta musamman domin nuna girmamawa a gare su.

An shirya wa ‘yan tattakin kaɓakin abinci a ofishin Rarara

Sai abin da jama’a da dama su ke cewa shi ne babu wani tabbas da ya nuna ko a ƙasa matasan su ka zo Kano kamar yadda aka san sauran masu yin tattaki na yi. 

Haka kuma tattaki irin wannan ba wani sabon abu ba ne ko abin burgewa a ƙasar nan ganin yadda abin ya zamo ruwan dare wanda har ta sa wasu ma idan aka fara yi masu tattakin sai su ce mai yin ya koma, ba sa buƙata.

Akwai ma masu kallon abin a matsayin tallar kai da neman abin duniya.

Idan kun tuna, shi kan sa babban mai taimaka wa Rarara a ɓangaren soshiyal midiya, Malam Rabi’u Garba Gaya, ya faɗa wa mujallar Fim a farkon tattakin matasan biyu cewa maigidan nasa ba zai karɓe su ba idan sun iso.

Ya ce: “Magana ta gaskiya, ko sun zo ba na tsammanin za a karɓe su, duba da yadda matasa yanzu sun ɗauki wannan abu a matsayin sana’a. Gaskiya dalilin kenan.

“Sannan kuma wataƙila lokacin da za su iso garin ma ba ya nan, tunda har yanzu ba ya nan.”

Loading

Tags: Aisha Ahmad IdrisAnas M. LawanAyshatulhumairaDauda Kahutu RararaKannywoodmawakaMustapha Iliyasutattakiziyara
Previous Post

Zaɓen 2023: Fiye da mutane miliyan 3 za su yi zaɓe a sansanin ‘yan gudun hijira – INEC

Next Post

Gwamnatin Kano ta bayyana matsayin ta kan batun Ado Gwanja, Safara’u da Mr. 442

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Isma'il Na'abba (Afakallahu)

Gwamnatin Kano ta bayyana matsayin ta kan batun Ado Gwanja, Safara'u da Mr. 442

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!