• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Kano ta bayyana matsayin ta kan batun Ado Gwanja, Safara’u da Mr. 442

by DAGA ABBA MUHAMMAD
September 10, 2022
in Labarai
0
Isma'il Na'abba (Afakallahu)

Isma'il Na'abba (Afakallahu)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Jihar Kano a yau ta bayyana matakin da ta ɗauka a game da maganar waƙar ‘Warr’ ta Ado Gwanja da waƙoƙin da bidiyoyin da mawaƙan nan Safara’u da Mr. 442 ke saki a soshiyal midiya.

Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Malam Isma’il Na-Abba (Afakallahu), shi ne ya bayyana matsayin gwamnatin a wata hira da ya yi da mujallar Fim a yau.

A hirar, Afakallahu ya ce hukumar sa ce ta farko wurin ɗaukar mataki kan Gwanja tun lokacin da wani lauya ya aika masu da takardar mai buƙatar cewa su dakatar da sakin sabuwar waƙar tasa ta ‘Warr’.

Ya ce: “Lokacin da lauyoyi su ka rubuto ƙorafi, sun rubuto wa Hukumar Tace Finafinai. Da su ka rubuto wa Hukumar Tace Finafinai, sai mu ka kirawo shi Ado Gwanja domin ya zo. A lokacin sai ya ce ba ya nan, ya na kan hanyar zuwa Ghana. To, lokacin na ba da umarnin a faɗa masa idan ya dawo ya zo, sannan kuma ya dakatar da sakin wannan waƙar saboda akwai ƙorafi a kan ta.

“Wannan shi ne abin da mu ka tsaya da shi a wannan lokacin. Amma mun samu labarin zuwan sa Ghana ya saki wannan waƙa. Don haka wannan matakin da mu ka ɗauka kenan dangane da wannan.

“Da ma kuma ita hukuma mataki-mataki ce,  daga wannan za a ɗauki mataki na gaba. Da ma kuma mu na shirin ɗaukar matakin don ganin an ƙare, kuma mu tsirar da mutuncin mutanen jihar mu ta Kano tunda hurumin mu Kano ne.”

Da ya ke bayani kan lamarin Safiyya Yusuf (Safara’u) da Mubarak Abdulkarim (Mr. 442), shugaban ya ce, “Su su Safara’u mun gayyace su, amma sun ce ba su nan. Amma mun yi hira da gidan Rediyon Freedom mun kai masu ‘open invitaion’, kuma mun ce su zo.

“Akwai waɗannan waƙoƙi da irin waɗannan abubuwan da su ke saki na rashin ta-ido, ba don wani abu ba. 

“Kuma kamar  shi shugaban nasu, Mr. 442, ya nuna cewa ba a gayyace su ba, amma in an gayyace su za su zo. To kuma mun ba su ‘open invitation’, tunda faɗa su ka yi a gidan rediyo, kuma ‘yan gidan rediyo su ka kira mu su ka yi ‘balancing’, sai mu ma mu ka ce ga matsayar mu, mu na ƙara ba su goron gayyata.”

Afakallahu ya ce ba manufar hukumar sa ba ne ta hukunta mutum ba bisa ƙa’ida ba. Ya ce: “Ba burin mu ba ne ko mu kora, ko mu ɗaure ko mu yi wani abu. Burin mu ne mu ga cewa mun kawo tsafta da gyara a kan waɗannan abubuwan na adabi, musamman waƙe-waƙen nan da ake yi da sauran su. 

Ado Gwanja (a hagu) da Safara’u da Mr. 442

“Saboda duk wanda ya ga wannan abu yadda ya ke, babu wanda zai bar waɗannan abubuwa a yadda su ke tafiya; dole a ce an yi waɗannan gyararraki da sauran su. Wannan shi ne abin da aka yi.

“Wancan kuma wani mataki ne da ita Hukumar Kula da Gidajen Rediyo Da Talbijin ta ɗauka don  hukunta shi Ado. Sannan ta ɗaya ɓangaren, su waɗancan lauyoyi sun kai ƙara a ‘Shari’a Court’ ta Ɗambatta, wanda alƙali ya ba da umarnin cewa ‘yan sanda su binciki waɗannan abubuwa da sauran su.”

Da mujallar Fim ta tambayi Afakallahu idan akwai wani mataki da hukumar sa ta ɗauka na ganin duk wanda ya yi waƙa kafin ya sake ta sai ya kawo wa hukumar ta tace, sai ya amsa da cewa, “Ai da ma aikin hukumar kenan. Amma abin ne ya zama cewa yanzu idan ka na Abuja za ka saki waƙa, mu kuma hurumin mu iya Kano ne, sai mu kare iya mutanen Kano. 

“Ma’ana, ba za mu bari ‘yan ‘downloading’ su yi ‘downloading’ ba, ba za mu bari ‘yan gidajen kallo su haska ba, ba za mu bari a sa mana a gidajen bukukuwa ba, sannan kuma in ba ka yarda da tsarin Kano ba, ba za mu bari kai ma ka zo ka yi ‘performance’ a Kano ba, domin mu na da ‘values’ na ‘culture’ da ‘religion’ ɗin mu.”

Loading

Tags: AfakallahubatsaIsma'il Na'abbaKanoMr 442Mubarak AbdulkarimSafara'uSafiyya Yusuf
Previous Post

Masu tattakin Rarara daga Kaduna sun isa Kano

Next Post

Mawaƙi Ɗan Musa Gombe zai angwance

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Ɗan Musa da katin gayyatar auren sa

Mawaƙi Ɗan Musa Gombe zai angwance

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!