• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 11, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Minista Idris ya ƙaddamar da yekuwar wayar da kan ɗalibai kan kafofin sadarwa

by ABUBAKAR IBRAHIM
May 10, 2025
in Nijeriya
0
Minista Idris ya ƙaddamar da yekuwar wayar da kan ɗalibai kan kafofin sadarwa

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, yana gabatar da jawabi a makarantar Nigerian Tulip International College a Abuja ranar Asabar

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da kamfen na wayar da kan ɗaliban makarantun sakandare kan kafofin sadarwa da yadda ake amfani da su ta hanyar da ta dace.

Da yake jawabi a taron TEDxNTICAbujaYouth 2025 da aka gudanar a makarantar Nigerian Tulip International College, Abuja, a ranar Asabar, ministan ya jaddada yadda kafafen sada zumunta suke da tasiri ga matasa, tare da buƙatar koya masu dabarun tantance sahihancin bayanan da suke karantawa da watsawa a intanet.

Ya ce: “Saboda ina cikin harkar sadarwa, na kasance mai matuƙar sha’awar yadda mutane suke yaɗa labarai, da yadda mutane za su iya sadar da juna cikin ɗan lokaci kaɗan daga ko’ina cikin duniya, sannan kafin mu ankara sai ga sararin sadarwar dijital ya buɗe. Yanzu akwai Instagram, Facebook, WhatsApp, X da sauran su, amma kuma wannan ma wani ƙalubale ne. Yanzu sadarwa maimakon ta zama abin haɗin kai, tana iya zama abin da za a yi amfani da ta ta hanya mara kyau.”

Ya ƙara da cewa, “Haɓakar duniyar dijital ita ma ta kawo zamanin yaɗa labaran ƙarya, da ruɗani da yaɗa bayanan da ba su da tushe.”

Da yake magana kan jigon taron mai taken “Shauƙi”, Idris ya ba da tarihin rayuwar sa, inda ya bayyana irin shauƙin da ya ke da shi tun yana matashi wajen zama ɗan jaridar gidan rediyo ko talbijin, sai dai wata matsala a gidan su ta tilasta masa shiga jami’a kafin ya cimma burin sa.

Ya ce: “A yau ni ne Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Nijeriya. Ba kawai ɗan watsa shirye-shirye ba ne ni, ni ne babban mai magana da yawun gwamnatin Nijeriya.

“Don haka za ka ga yadda burin da ake ganin kamar an kashe shi shekaru da dama da suka wuce, ya dawo ya amfanar.”

Ya ce kafin ya zama minista, ya mallaki tashar rediyo da talbijin har ma da gidan jarida.

Ministan ya buƙaci matasa da kada su yi watsi da burin su ko da ba sa ganin damar cimma buƙatar su. Ya ce shauƙin sa ne yake motsa shi wajen yaƙi da yaɗuwar labaran ƙarya ta hanyar ƙarfafa fahimtar kafofin sadarwa.

Idris ya kuma bayyana cewa daga watan Nuwamba mai zuwa, Nijeriya za ta fara gudanar da Cibiyar Ilimin Kafofin Sadarwa ta UNESCO mai Mataki na 2.

Ya ce: “Ni ne na jagoranci Nijeriya wajen kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Sadarwa ta UNESCO Category 2 – wadda ita ce irin ta ta farko a duniya – kuma za a kafa ta a Abuja. Zuwa watan Nuwamba idan hukumar UNESCO ta bayar da amincewar ƙarshe, duk duniya za ta dinga kallon Nijeriya.”

Ya ƙara da cewa, “Don haka ba wai kawai ku matasa maza da mata ku ɗauki makirfo, kwamfuta ko wayoyin ku na zamani ku fara faɗin duk abin da kuka ga dama ba ne. Kuna iya samun ilimi, amma kuma kuna buƙatar fahimtar yadda kafofin sadarwa suke.”

An tsara cibiyar ne don koyar da matasa daga Nijeriya da ƙasashen waje dabarun amfani da kafofin sadarwa cikin basira tare da yin kaffa-kaffa da kuma kare kan su daga labaran ƙarya da yaɗuwar bayanan da ba su da tushe.

Loading

Previous Post

Ƙungiyar Sadarwa ta Ƙasa ta kammala bitar ayyukan ta, ta fitar da sababbin matakan tallata nasarorin gwamnatin Tinubu

Next Post

Tinubu ya yaba wa Sule Lamiɗo a taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Tinubu ya yaba wa Sule Lamiɗo a taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa

Tinubu ya yaba wa Sule Lamiɗo a taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!